Close Menu
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • Hajj News
  • Global
  • Health
  • Nahcon
  • Picture Gallery
  • Opinion
  • Videos
  • HAUSA
Facebook X (Twitter) Instagram
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram
SUBSCRIBE
  • Home
  • Hajj News

    Sheikh Adamu Dokoro Urges Nigerian Pilgrims in Madina to Follow Prophetic Teachings

    May 24, 2025

    975 Kwara Pilgrims Airlifted for 2025 Hajj

    May 15, 2025

    First Hajj Pilgrims Arrive by Sea at Jeddah Islamic Port

    May 15, 2025

    Nigerian Pilgrims Begin Second Phase of 2025 Hajj Journey – By Aminu Kabir Muhammad

    May 14, 2025

    Niger State’s First Batch of Pilgrims Set for Airlift to Saudi Arabia

    April 30, 2025
  • Global

    flyadeal Aims To Serve 75,000 International Hajj Pilgrims In 2025

    January 23, 2025

    Reflections on the 4th Hajj Conference and Exhibition in Jeddah – By Muhammad Ahmad Musa

    January 21, 2025

    Hajj and Umrah Expo 2025: Innovation and Collaboration Take Center Stage in Jeddah – By Fatima Sanda Usara

    January 14, 2025

    Makkah Red Crescent Boosts Preparedness to Heavy Rainfall

    January 6, 2025

    Intense Rainfall Sweeps Through Makkah, Madina and Jeddah

    January 6, 2025
  • Health

    Gombe Muslim Pilgrim Board Commences Vaccination for 2025 Hajj Pilgrims – By Abdulqadir Aliyu Shehu

    April 28, 2025

    NAHCON Inaugurates Committee To Review National Medical Team Guidelines for Hajj 2025

    December 19, 2024

    Saudi Health Minister Strengthen Ties With Greece On Health Cooperation During Official Visit

    November 23, 2024

    Umm Al-Qura University volunteers extend help to pilgrims in Mina during Tashreeq

    June 17, 2024

    Hajj 2024: African pilgrim airlifted for emergency care

    June 14, 2024
  • Nahcon

    NAHCON Intensifies Efforts in Makkah to Fast-Track Nusuk Card Distribution for Nigerian Pilgrims

    May 22, 2025

    NAHCON Chairman Tasks Media Team on Fair, Responsible Coverage of 2025 Hajj

    May 20, 2025

    NAHCON Steps Up Oversight of Tour Operators’ Catering Ahead of 2025 Hajj

    May 19, 2025

    NAHCON Chairman Applauds Madinah Operations Team, Hails Stakeholder Collaboration

    May 18, 2025

    NAHCON Ensures Quality Feeding for Over 17,000 Nigerian Pilgrims in Madinah – By Ahmad Mu’azu

    May 16, 2025
  • Picture Gallery
  • Opinion

    Exposing Leadership Newspaper’s many lies against NAHCON chairman – By Ahmad Shafi’i PhD

    May 8, 2025

    What Do the Enemies of NAHCON Chairman Really Want? 

    May 3, 2025

    Who Will Now Thank the NAHCON Chairman? By Assalafy Yola

    April 29, 2025

    Hajj Commission, Professor Abdallahi Saleh, VP Shettima and the Daily Nigerian Report – By Uncle Anas Dukura

    April 18, 2025

    Who Is After the NAHCON Chairman? By Assalafy Yola

    April 9, 2025
  • Videos
  • HAUSA
HAJJ CHRONICLES
Home » Hankalin Shugaban Hukumar NAHCON Bai Tashi Ba, Kuma Bai Girgiza Ba, Ya Himmatu Wajen Tabbatar Da Tsantsaini A Ayyukan Hajji – Daga Nura Ahmad Dakata 
Hausa

Hankalin Shugaban Hukumar NAHCON Bai Tashi Ba, Kuma Bai Girgiza Ba, Ya Himmatu Wajen Tabbatar Da Tsantsaini A Ayyukan Hajji – Daga Nura Ahmad Dakata 

adminBy adminFebruary 13, 2025No Comments4 Mins Read
Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Email Telegram
FB IMG 1739398212000

Yayin da ake kokarin bata masa suna a baya-bayan nan, Shugaban Hukumar Alhazai ta Najeriya (NAHCON), Farfesa Abdullahi Saleh Usman, ya ci gaba da jajircewa wajen ganin an tabbatar da gaskiya da rikon amana a ayyukan Hajji. 

 

Da yake mayar da martani game wani labara da wasu bata-gari ke yadawa da nufin bata sunan shugabancin NAHCO, Kodinetan kungiyar tallafawa alhazan Najeriya ta kafafen yada labarai na shiyyar Kano da Jigawa, Nura Ahmad, ya tabbatar da cewa “Babu wani batanci da zai sa shugaban hukumar NAHCON ya kauce daga babbar manufarsa ta tabbatar da gaskiya da rikon amana a ayyukan Hajji.”

 

A makonnin da suka gabata ne dai wasu zarge-zarge da ba su da tushe suka taso, inda aka yi karyar cewa Shugaban Hukumar NAHCON shi daya ya soke kwangilar da Hukumar ta yi da kamfanin dake yi wa alhazai hidima a Saudiyya, wanda hakan zai kawo cikas ga Alhazan Najeriyar a aikin Hajjin 2025.

 

Wannan ikirari dai mutane da yawa sun musanta shi daga hukumar NAHCON da masu ruwa da tsaki a aikin Hajji, wadanda suka tabbatar da cewa duk yarjejeniyoyin suna nan daram, kuma shirye-shiryen aikin hajjin na tafiya yadda ya kamata.

 

Farfesa Usman ya musanta wadannan tuhume-tuhume da kakkausar murya, musamman ikirarin da kungiyar shugabannin hukumomin jin dadin alhazai na jihohi suka yi kan cewa shi kadai ya soke kwangilar masu hidimar ba tare da tuntubarsu ba.

 

Ya kalubalanci wadanda ke wannan zargi da su bayar da kwararan hujjoji da za su tabbatar da ikirarin nasu, inda ya kara da cewa ba a yanke wani muhimmin hukunci dangane da ayyukan Hajji ba tare da tuntubar shugabannin kungiyar ba.

 

“Idan suna da wata hujja, to su gabatar da ita ga jama’a. NAHCON tana gudanar da aiki cikin gaskiya, kuma duk shawarar da aka yanke game da masu yi wa alhazai hidima an yi ne bisa bin ka’ida,” ya bayyana hakan a wata hira da ya yi da DCL Hausa.

 

Da yake karin haske kan ziyarar aikin da yake ci gaba da yi zuwa Saudiyya, Farfesa Usman ya bayyana cewa ya yi wata ganawa da ma’aikatansa na Makkah, inda suka yi masa bayani kan muhimman batutuwan da suka shafi shirye-shiryen Hajjin bana.

 

“Muna da wani taro da ma’aikatar Hajji da Umrah ta Saudiyya. Mun zo nan don fayyace batutuwa masu cin karo da juna dangane da masu ba da sabis. Ba za mu iya naɗe hannayenmu kawai mu ƙyale ƙoƙarinmu ya zama a banza ba,” Shugaban ya jaddada hakan

 

Shugaban ya kara da tabbatar wa alhazai da masu ruwa da tsaki cewa duk yarjejeniyoyin kwangilar suna nan daram sannan kuma shawarar da NAHCON ta yanke a koda yaushe yana da amfani ga alhazan Najeriya.

 

Ya ci gaba da cewa, “muna mayar da hankali ne kan ganin cewa alhazan Najeriya sun samu ingantattun hidimomi a farashi mai sauki. Ba za mu shagaltu da zarge-zargen da ba su da tushe balle makama ba.”

 

Masu kishin bunkasa walwalar alhazai da suka hada da Kungiyar ‘Yan jaridu masu Tallafawa Alhazan Najeriya (NHMST), sun yi kira ga al’umma da su yi watsi da wannan mummunan labari, suna masu bayyana hakan a matsayin wani yunkuri na masu zagon kasa na haifar da firgici na babu gaira ba dalili a cikin harkar Hajji.

 

“Wadannan labaran karya aikin wasu mutane ne da ke neman yin amfani da tsarin don biyan bukatun kansu,” in ji Kodinetan NHMST na kasa, Ibrahim Abubakar Nagarta, a wata sanarwa da ya fitar kwanan nan.

 

Duk da wannan kalubalen, NAHCON ta ci gaba da jajircewa wajen ganin an gudanar da aikin Hajji mai inganci ga alhazan Najeriya.

 

Hukumar karkashin jagorancin Farfesa Abdullahi Saleh Usman ta baiwa masu ruwa da tsaki tabbacin cewa za a ci gaba da yada bayanai kan aikin Hajjin 2025 ta hanyoyin da aka tabbatar.

 

A yayin da ake ci gaba da shirye-shiryen gudanar da aikin Hajin 2025, masu ruwa da tsaki sun bukaci hadin kai tare da mai da hankali kan hadafin hadin gwiwa na inganta ayyukan Hajjin Najeriya maimakon barin abubuwan da za su kawo cikas ga ci gabansa.

Farfesa Abdullahi Saleh Usman Hajj 2025 Shugaban NAHCON
Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp

Related Posts

NAHCON Intensifies Efforts in Makkah to Fast-Track Nusuk Card Distribution for Nigerian Pilgrims

May 22, 2025

NAHCON Chairman Tasks Media Team on Fair, Responsible Coverage of 2025 Hajj

May 20, 2025

Governor Inuwa Yahaya Bids Farewell to First Batch of Gombe Pilgrims for 2025 Hajj – By Abdulkadir Aliyu Shehu

May 19, 2025
Leave A Reply Cancel Reply

Don't Miss
Hajj News

Sheikh Adamu Dokoro Urges Nigerian Pilgrims in Madina to Follow Prophetic Teachings

By adminMay 24, 20250

Renowned Islamic scholar, Sheikh Adamu Muhammad Dokoro, has urged Nigerian intending pilgrims currently in Madina…

NAHCON Intensifies Efforts in Makkah to Fast-Track Nusuk Card Distribution for Nigerian Pilgrims

May 22, 2025

NAHCON Chairman Tasks Media Team on Fair, Responsible Coverage of 2025 Hajj

May 20, 2025

NAHCON Steps Up Oversight of Tour Operators’ Catering Ahead of 2025 Hajj

May 19, 2025
Stay In Touch
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • WhatsApp
Our Picks

Sheikh Adamu Dokoro Urges Nigerian Pilgrims in Madina to Follow Prophetic Teachings

May 24, 2025

NAHCON Intensifies Efforts in Makkah to Fast-Track Nusuk Card Distribution for Nigerian Pilgrims

May 22, 2025

NAHCON Chairman Tasks Media Team on Fair, Responsible Coverage of 2025 Hajj

May 20, 2025

NAHCON Steps Up Oversight of Tour Operators’ Catering Ahead of 2025 Hajj

May 19, 2025
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
© 2025HAJJ CHRONILES

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.