Close Menu
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • Hajj News
  • Global
  • Health
  • Nahcon
  • Picture Gallery
  • Opinion
  • Videos
  • HAUSA
Facebook X (Twitter) Instagram
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram
SUBSCRIBE
  • Home
  • Hajj News

    2026/1447 Hajj Preparations Officially Launched as NAHCON Joins Global Pilgrimage Community in Closing Ceremony

    June 9, 2025

    No Lives Lost in Makkah Fire, Senate Foreign Affairs Committee Confirms

    June 9, 2025

    Pilgrimage and Leadership: How Governor Inuwa Yahaya Stood Tall Among His Peers During the 2025 Hajj – Abdulkadir Aliyu Shehu

    June 8, 2025

    From Crisis to Victory: NAHCON Chairman Called to Prostrate in Thanks for 2025 Hajj Breakthrough – By Shamwil Isah

    June 8, 2025

    Governor Abba Yusuf Disburses ₦361 Million Support to Kano Pilgrims in Mina

    June 8, 2025
  • Global

    Indonesia Plans to Acquire Land for Hajj Village Near Makkah’s Grand Mosque

    July 31, 2025

    Egypt To Halt Land Hajj Trips by 2026 Over Saudi Transport Policy Changes

    July 31, 2025

    UAE Unveils Streamlined Hajj 2026 Accreditation Process to Ensure Transparency and Quality

    July 24, 2025

    flyadeal Aims To Serve 75,000 International Hajj Pilgrims In 2025

    January 23, 2025

    Reflections on the 4th Hajj Conference and Exhibition in Jeddah – By Muhammad Ahmad Musa

    January 21, 2025
  • Health

    Gombe Muslim Pilgrim Board Commences Vaccination for 2025 Hajj Pilgrims – By Abdulqadir Aliyu Shehu

    April 28, 2025

    NAHCON Inaugurates Committee To Review National Medical Team Guidelines for Hajj 2025

    December 19, 2024

    Saudi Health Minister Strengthen Ties With Greece On Health Cooperation During Official Visit

    November 23, 2024

    Umm Al-Qura University volunteers extend help to pilgrims in Mina during Tashreeq

    June 17, 2024

    Hajj 2024: African pilgrim airlifted for emergency care

    June 14, 2024
  • Nahcon

    NAHCON, Private Tour Operators Hold Virtual Meeting to Streamline 2026 Hajj Operations – By Aminu Kabir

    October 8, 2025

    NAHCON Applauds President Tinubu, VP Shettima for Directive to Cut 2026 Hajj Cost

    October 7, 2025

    2026 Hajj: NAHCON Kicks Off Verification of Licensed Tour Operators – By Shafii Sani Mohammed

    October 6, 2025

    Pilgrims to Benefit as Tinubu, Shettima Secure Lower Hajj Costs – NAHCON Chairman

    October 2, 2025

    NAHCON Chairman Felicitates Nigerians on Independence Day

    October 1, 2025
  • Picture Gallery
  • Opinion

    Tinubu’s Hajj Fare Directive Aligns with NAHCON Chairman’s Vision for Affordable Pilgrimage – By Sirajo Salisu Jibia

    October 8, 2025

    Opinion: President Tinubu Is Right to Instruct NAHCON to Review and Cut Hajj Fares – By Muhammad Sulaiman Gama

    October 8, 2025

    Supporting NAHCON chairman’s leadership – By Raji Saidu Onipson

    September 17, 2025

    Hajj Pilgrimage and Misconception Over Funding – By Raheem Akingbolu

    August 27, 2025

    Prof. Abdullahi Saleh Usman: The Erudite Reformer Steering NAHCON Towards Excellence

    July 15, 2025
  • Videos
  • HAUSA
HAJJ CHRONICLES
Home » Umarnin Shugaba Tinubu Kan Rage Farashin Hajji Yayi Daidai Da Manufar Shugaban NAHCON Na Samar Da Arha Ga Maniyyata – Sirajo Salisu Jibia
Hausa

Umarnin Shugaba Tinubu Kan Rage Farashin Hajji Yayi Daidai Da Manufar Shugaban NAHCON Na Samar Da Arha Ga Maniyyata – Sirajo Salisu Jibia

adminBy adminOctober 8, 2025No Comments4 Mins Read
Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Email Telegram
IMG 20250928 WA0010

Umarnin da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya bayar kwanan nan ga Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON) da ta gaggauta sake duba farashin kujerar Hajjin shekarar 2026 tare da rage shi, wani babban ci gaba ne da ya dace da manufar Shugaban Hukumar, Farfesa Abdullahi Saleh Usman, wanda burinsa tun farko shi ne tabbatar da cewa aikin Hajji ya kasance mai araha ga dukkan Musulman Najeriya.

Umarnin Shugaban Kasa ya bukaci NAHCON da ta sake lissafa farashin kujerun Hajji domin ya nuna yadda Naira ta samu karuwa a kan Dala.

Wannan mataki na gwamnati ya zo a kan gaba, yana ceton maniyyatan Najeriya daga tsadar kujerar da aka sanar da ita tun farko, wadda aka kirga bisa “hasashen sauyin kudi na N1,550 a kan Dala daya. Farashin farko ya kasance tsakanin N8.1m zuwa N8.5m bisa ga yankuna daban-daban.

Ana sa ran sabon umarnin zai rage farashin zuwa kusan tsakanin N7.6m da N7.7m.

Murnar da Shugaban NAHCON ya nuna kan wannan labari abin fahimta ne, domin ya tabbatar da jajircewarsa wajen rage farashi da kula da walwalar maniyyata.

Tun daga lokacin da ya hau Shugabancin hukumar, Farfesa Saleh Usman ya sanya araha da ingantacciyar hidima ga maniyyata a matsayin babban ginshikin aikinsa.

Ko da yake sabon yinkurin rage farashin ya samo asali ne daga karfin Naira, ya ginu ne kan matakan rage kudi da shugabancin NAHCON ya riga ya dauka tun da farko.

Daya daga cikin manyan nasarorin da shugabancin ya cimma shi ne tanadin rangwame ga maniyyata ta hanyar samun saukin farashin hidima da ya kai kimanin Naira biliyan 19 gaba daya. An cimma hakan ne bayan samun rangwamen fiye da N200,000 kan kowane maniyyaci daga wurin masu yin hidima ga Alhazai a Saudiyya, abin da ya zama babban tanadi ga kusan maniyyata 66,000 da aka warewa Najeriya.

Wani babban abin alfahari kuma shi ne yadda NAHCON ta inganta tsarin kwangiloli, wanda ya taka rawar gani wajen nasarar aikin Hajjin 2025.

A wancan lokacin, tawagar Farfesa Saleh Usman ta yi gyara kan kwangilolin ayyuka domin su dace da adadin maniyyatan da aka yi rajista, mataki wanda ya hana asarar kudi da yawa kuma ya taimaka wajen rage farashin kujerar.

NAHCON kuma ta fadada tsarin Hajj Savings Scheme, inda shugaban ya kara karfafa tsarin ta hanyar hada kai da karin bankuna domin karfafa al’adar ajiya tun da wuri, don rage wahalar biyan kudi da lokaci daya.

Sai dai duk wadannan nasarori ba su samu ba tare da kalubale ba. Kudurinsa na samar da hidimomi masu inganci da araha ya taba shiga rikici da wasu masu muradun kansu.

Rahotanni na nuna cewa tsadar da aka bayyana a farko na iya da nasaba da matsin lamba daga wasu bangarori da ke da hannu a harkar kwangila, musamman batun zaben kamfani daya tilo da zai rika gudanar da ayyukan din Hajji.

Manufar Farfesa Saleh Usman tun farko ita ce a dauki kamfanoni da dama masu inganci domin gudanar da ayyuka, domin hakan zai haifar da gasa mai kyau wadda za ta rage kudi kuma ta inganta sabis ga maniyyata. Saboda haka, wannan umarnin Shugaban Kasa ya zama tamkar karfafa guiwa da kuma damar da za ta bashi damar kaucewa duk wata cikas ta son kai ko na birokrasiya wajen cimma manufar rage farashi bisa mafi kyawun canjin kudi.

Domin cika wannan buri, Shugaban NAHCON yana kokarin karfafa al’adar biyan kudi da wuri. Ya bukaci Jihohin da ke da Hukumar Jin Dadin Alhazai su tabbatar da cewa suna aika kudin maniyyata cikin lokaci.

Wannan yana da matukar muhimmanci domin hakan zai bai wa Babban Bankin Kasa (CBN) damar sayen kudin kasashen waje bisa farashin da ya inganta, wanda hakan zai tabbatar da ajiye kudi ga maniyyata.

An sanya ranar karshe ta biyan kaso 50% na kudin Hajji a ranar 8 ga Oktoba, 2025, yayin da cikakken biyan kudin zai kare a ranar 31 ga Disamba, 2025.

A fili yake cewa Farfesa Abdullahi Saleh Usman yana kan hanya madaidaiciya wajen gudanar da daya daga cikin ayyukan Hajji mafi nasara da araha a tarihin Najeriya. Jajircewarsa kan amfani da kudi cikin hikima tare da goyon bayan fadar Shugaban Kasa na nuna alamar cewa aikin Hajjin 2026 zai kasance mai tarihi wanda zai tabbatar da manufar samun sauki da ingantaccen sabis ga maniyyata.

Sirajo Salisu Jibia
Ya rubuta daga Japan.

Kudin Haji Shugaba Tinubu Shugaban NAHCON
Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp

Related Posts

Kiyasin NAHCON: Darussa Daga Abubuwan Da Suka Gabata

October 7, 2025

Maimaita Kiran Shugaban NAHCON Kan Cire Harajin Kashi 2 Cikin 100 Da CBN Ke Yi A Kudin Kujerar Haji – AHMSP

October 7, 2025

Shugaban NAHCON Yaba Da Umarnin Fadar Shugaban Kasa Kan Rage Kudin Hajji Na Shekarar 2026 – AHMSP

October 7, 2025
Leave A Reply Cancel Reply

Don't Miss
Kano Pilgrims Board

FAAN Presents Award of Excellence to Kano Pilgrims Board DG

By adminOctober 9, 20250

The Federal Airports Authority of Nigeria (FAAN) has honoured the Director General of the Kano…

Umarnin Shugaba Tinubu Kan Rage Farashin Hajji Yayi Daidai Da Manufar Shugaban NAHCON Na Samar Da Arha Ga Maniyyata – Sirajo Salisu Jibia

October 8, 2025

Tinubu’s Hajj Fare Directive Aligns with NAHCON Chairman’s Vision for Affordable Pilgrimage – By Sirajo Salisu Jibia

October 8, 2025

NAHCON, Private Tour Operators Hold Virtual Meeting to Streamline 2026 Hajj Operations – By Aminu Kabir

October 8, 2025
Stay In Touch
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • WhatsApp
Our Picks

FAAN Presents Award of Excellence to Kano Pilgrims Board DG

October 9, 2025

Umarnin Shugaba Tinubu Kan Rage Farashin Hajji Yayi Daidai Da Manufar Shugaban NAHCON Na Samar Da Arha Ga Maniyyata – Sirajo Salisu Jibia

October 8, 2025

Tinubu’s Hajj Fare Directive Aligns with NAHCON Chairman’s Vision for Affordable Pilgrimage – By Sirajo Salisu Jibia

October 8, 2025

NAHCON, Private Tour Operators Hold Virtual Meeting to Streamline 2026 Hajj Operations – By Aminu Kabir

October 8, 2025
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
© 2025HAJJ CHRONILES

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.