Close Menu
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • Hajj News
  • Global
  • Health
  • Nahcon
  • Picture Gallery
  • Opinion
  • Videos
  • HAUSA
Facebook X (Twitter) Instagram
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram
SUBSCRIBE
  • Home
  • Hajj News

    2026/1447 Hajj Preparations Officially Launched as NAHCON Joins Global Pilgrimage Community in Closing Ceremony

    June 9, 2025

    No Lives Lost in Makkah Fire, Senate Foreign Affairs Committee Confirms

    June 9, 2025

    Pilgrimage and Leadership: How Governor Inuwa Yahaya Stood Tall Among His Peers During the 2025 Hajj – Abdulkadir Aliyu Shehu

    June 8, 2025

    From Crisis to Victory: NAHCON Chairman Called to Prostrate in Thanks for 2025 Hajj Breakthrough – By Shamwil Isah

    June 8, 2025

    Governor Abba Yusuf Disburses ₦361 Million Support to Kano Pilgrims in Mina

    June 8, 2025
  • Global

    Indonesia Plans to Acquire Land for Hajj Village Near Makkah’s Grand Mosque

    July 31, 2025

    Egypt To Halt Land Hajj Trips by 2026 Over Saudi Transport Policy Changes

    July 31, 2025

    UAE Unveils Streamlined Hajj 2026 Accreditation Process to Ensure Transparency and Quality

    July 24, 2025

    flyadeal Aims To Serve 75,000 International Hajj Pilgrims In 2025

    January 23, 2025

    Reflections on the 4th Hajj Conference and Exhibition in Jeddah – By Muhammad Ahmad Musa

    January 21, 2025
  • Health

    Gombe Muslim Pilgrim Board Commences Vaccination for 2025 Hajj Pilgrims – By Abdulqadir Aliyu Shehu

    April 28, 2025

    NAHCON Inaugurates Committee To Review National Medical Team Guidelines for Hajj 2025

    December 19, 2024

    Saudi Health Minister Strengthen Ties With Greece On Health Cooperation During Official Visit

    November 23, 2024

    Umm Al-Qura University volunteers extend help to pilgrims in Mina during Tashreeq

    June 17, 2024

    Hajj 2024: African pilgrim airlifted for emergency care

    June 14, 2024
  • Nahcon

    NAHCON Approves Two 23kg Checked Bags for 2026 Hajj Pilgrims

    January 1, 2026

    NAHCON Begins Preparations for 2026 Hajj Medical Operations

    December 30, 2025

    No Contract Rollover: NAHCON Sets Record Straight on 2026 Hajj Procurement

    December 18, 2025

    The Penumbra of Influence: How Mercenary Journalism Built False Narratives Around NAHCON By Ahmad Mu’azu

    December 16, 2025

    NAHCON Opens Application Portal for 2026 National Medical Team

    December 12, 2025
  • Picture Gallery
  • Opinion

    The Need to Reintroduce Capacity-Building Workshops for Hajj Information Managers in Nigeria By Faruku Umar

    January 13, 2026

    Integrity, Discipline and Tireless Communication: Kano Pilgrims Board Shines Under Dedicated Leadership

    January 13, 2026

    NAHCON At 20: The Imperative of Repositioning Nigeria’s Hajj and Umrah Sector – Ibrahim Ishaq Jae

    January 12, 2026

    2026 Hajj Crisis: NAHCON, GACA Set to Clash Over Pilgrims’ Airlift

    January 11, 2026

    Man of the year: Professor Abdullahi Saleh, the game Changer – By Sagir Huguma

    January 3, 2026
  • Videos
  • HAUSA
HAJJ CHRONICLES
Home » Gaskiya Ko Jita-Jita? Labarin Biliyan 50 da Aka Ce An Sace a NAHCON – Ganiyu Lamidi
Hausa

Gaskiya Ko Jita-Jita? Labarin Biliyan 50 da Aka Ce An Sace a NAHCON – Ganiyu Lamidi

adminBy adminOctober 12, 2025No Comments4 Mins Read
Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Email Telegram
FB IMG 1740752692759

A Najeriya, jita-jita kan zama kamar gaskiya idan aka yi ta maimaitawa. Labaran karya kan shafe na gaskiya, saboda mutane suna son jin labaran Al’ajabi, shakku ko mamaki. Mun taba jin labarin Madam Koi-Koi da Iliya dan Mai-Karfi, duk da ba gaskiya ba ne, amma mutane sun dade suna yada wannan labaran.

Yanzu haka, Hukumar Alhazan Najeriya, NAHCON, da Shugabanta Farfesa Abdullahi Saleh Usman, sun fada cikin irin wannan jita-jitar. Zargin wai an sace Naira biliyan 50 a hajjin da ya gabata. Labarin ya yadu Kamar wutar daji a kafafen sada zumunta da jaridu, amma babu wata hujja ko gaskiya cikin lamarin. Zargi ne kawai da ‘Yan siyasa ke kara rura wutarsa.

Idan muka duba lamarin a hankali, za mu ga cewa wannan magana bata da tushe. A 2025, alhazai daga kudanci sun biya kusan Naira miliyan 8.78, yayin da na arewa suka biya Naira miliyan 8.46. Idan aka raba Naira biliyan 50 da wannan farashi, zai bamu adadin alhazai kusan 5,700. Wato sai mutum ya karbi kudin alhazai fiye da dubu biyar da ba su tafi Hajji ba, ko kuma ya karkatar da kaso 12 na kudin dukkan alhazai suka Biya a kasar sannan hakan za ta iya kasancewa.

Irin wannan satar ba abu ne mai sauki ba. Domin sai NAHCON da masu jiragen sama da masu masauki da masu abinci, da hukumomin jihohi su hada baki lokaci guda, kafin a iya cin wadannan kudade.

Sai kuma a ce irin wannan kudi sun bata amma majalisar wakilai da fadar shugaban kasa su yi shiru gaba daya. Wannan kusan ba zai taba yiwuwa ba.

A yau, babu wata Shaida da ta nuna an saci irin wannan kudi. Babu wanda ya fito da takarda ko shaidar batan kudin. Babu kasafin kudi wato (budget) da ya nuna wani gibi na wannan kudade Amma kawai sai labari keta yaduwa, domin mutane na son jin irin wadannan jita-jita.

Abin da nake gani a  Najeriya ce kawai hakan ke faruwa. Idan sabon shugaba mai son ayi gyara ya hau, sai ya fara gyare gyare. Wadanda suka saba da tsohon tsarin sukan ji haushi, su fara yada jita-jita don su bata sunan sabon shugaban. Sai a shaci labarin teburin Mai Shanyi a  fitar da adadin kudi mai yawa kamar “biliyan 50” don ta tada hankali da kawo CeCe-kuce a tsakanin jama’a

Gaskiya, Farfesa Abdullahi Saleh Usman yana kokarin tsaftace aikin Hajji. Ya rage almundahana, ya kara tsari. Wadannan canje-canje suna bawa wasu ciwon kai, musamman wadanda suka saba cin moriyar tsohon tsarin.

Amma fa, wannan ba yana nufin kada ayi a bincike ba. Idan akwai laifi, a bincika a fito fili dashi. Mutane na da hakkin sanin gaskiya. Amma su ma Yan NAHCON suna da hakkin kada a zalunce su da jita-jita marar hujja.

Har yanxu Hukumar EFCC ma bata fitar da wata shaida ba. Babu rahoton da ya tabbatar da wannan zargi. Abin da ke yawo kawai shi ne maganar “an sace biliyan 50,”

NAHCON tana da lissafi. Ana iya duba adadin alhazai, kwangiloli, da kudade. Idan akwai rashin gaskiya, sai a gani a rubuce. Wannan shi ne ainihin hanyar bincike, ba hira a Facebook ko WhatsApp ba.

Madam Koi-Koi bata taba wanzuwa ba, amma har yanzu mutane na jin labarinta. Haka ma wannan labari na biliyan 50, ya yadu ne saboda mutane sun riga sun yarda cewa gwamnati tana cike da rashawa. Amma imani ba hujja ba ne. Kuma gwamnati ba za ta yi aiki a bisa zato cewa kowa barawo ba ne.

A bari masu bincike su gama aikinsu. A bari gaskiya ta fito fili. Jama’a su nemi gaskiya da adalci, domin duka biyun suna aiki tare.

Gaskiya tana da daraja fiye da jita-jita. Kada mu bar karya ta maye gurbin gaskiya.

Ganiyu Lamidi
Masani ne kan manufofin gwamnati da gyaran gudanarwa a Najeriya.

Kudin Haji Naira Biliyan Hamsin NHACON Tatsuniya
Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp

Related Posts

Nagarta, Da’a da Sadarwa Cikin Jajircewa: Hukumar Alhazan Kano na Haskakawa ƙarƙashin Jagoranci Nagari

January 13, 2026

Rikicin Jigilar Alhazan 2026: Zargin Makircin Cikin Gida A NAHCON Na Barazana Ga Yarjejeniyar Sufurin Jirage Tsakanin Najeriya Da Saudia

January 12, 2026

Hajjin 2026: Jihar Gombe Ta Fara Gwajin Lafiya na Tilas ga Maniyyatan – Daga Abdulkadir Aliyu Shehu

January 12, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

Don't Miss
SPWA

Hajj 2026: Lagos begins medical screening for intending pilgrims, appoints LGA coordinators

By adminJanuary 14, 20260

The Lagos State Government has commenced medical screening for all intending pilgrims performing the 2026…

Hajj 2026: Kano Pilgrims Board Announces Deadline for Data Capturing

January 14, 2026

The Need to Reintroduce Capacity-Building Workshops for Hajj Information Managers in Nigeria By Faruku Umar

January 13, 2026

Nagarta, Da’a da Sadarwa Cikin Jajircewa: Hukumar Alhazan Kano na Haskakawa ƙarƙashin Jagoranci Nagari

January 13, 2026
Stay In Touch
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • WhatsApp
Our Picks

Hajj 2026: Lagos begins medical screening for intending pilgrims, appoints LGA coordinators

January 14, 2026

Hajj 2026: Kano Pilgrims Board Announces Deadline for Data Capturing

January 14, 2026

The Need to Reintroduce Capacity-Building Workshops for Hajj Information Managers in Nigeria By Faruku Umar

January 13, 2026

Nagarta, Da’a da Sadarwa Cikin Jajircewa: Hukumar Alhazan Kano na Haskakawa ƙarƙashin Jagoranci Nagari

January 13, 2026
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
© 2026HAJJ CHRONILES

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.