Close Menu
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • Hajj News
  • Global
  • Health
  • Nahcon
  • Picture Gallery
  • Opinion
  • Videos
  • HAUSA
Facebook X (Twitter) Instagram
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram
SUBSCRIBE
  • Home
  • Hajj News

    2026/1447 Hajj Preparations Officially Launched as NAHCON Joins Global Pilgrimage Community in Closing Ceremony

    June 9, 2025

    No Lives Lost in Makkah Fire, Senate Foreign Affairs Committee Confirms

    June 9, 2025

    Pilgrimage and Leadership: How Governor Inuwa Yahaya Stood Tall Among His Peers During the 2025 Hajj – Abdulkadir Aliyu Shehu

    June 8, 2025

    From Crisis to Victory: NAHCON Chairman Called to Prostrate in Thanks for 2025 Hajj Breakthrough – By Shamwil Isah

    June 8, 2025

    Governor Abba Yusuf Disburses ₦361 Million Support to Kano Pilgrims in Mina

    June 8, 2025
  • Global

    Indonesia Plans to Acquire Land for Hajj Village Near Makkah’s Grand Mosque

    July 31, 2025

    Egypt To Halt Land Hajj Trips by 2026 Over Saudi Transport Policy Changes

    July 31, 2025

    UAE Unveils Streamlined Hajj 2026 Accreditation Process to Ensure Transparency and Quality

    July 24, 2025

    flyadeal Aims To Serve 75,000 International Hajj Pilgrims In 2025

    January 23, 2025

    Reflections on the 4th Hajj Conference and Exhibition in Jeddah – By Muhammad Ahmad Musa

    January 21, 2025
  • Health

    Gombe Muslim Pilgrim Board Commences Vaccination for 2025 Hajj Pilgrims – By Abdulqadir Aliyu Shehu

    April 28, 2025

    NAHCON Inaugurates Committee To Review National Medical Team Guidelines for Hajj 2025

    December 19, 2024

    Saudi Health Minister Strengthen Ties With Greece On Health Cooperation During Official Visit

    November 23, 2024

    Umm Al-Qura University volunteers extend help to pilgrims in Mina during Tashreeq

    June 17, 2024

    Hajj 2024: African pilgrim airlifted for emergency care

    June 14, 2024
  • Nahcon

    NAHCON Chairman Strengthens Ties with Saudi Embassy Ahead of 2026 Hajj

    February 27, 2026

    NAHCON Signs 2026 Hajj Airlift Agreement, Emphasizes Compliance and Efficiency

    February 25, 2026

    No Additional Slots for 2026 Hajj, Says NAHCON as Visa Issuance Nears

    February 24, 2026

    NAHCON Unveils Reforms, Clarifies Quota Adjustment Ahead of 2026 Hajj – By Abdulbasit Abba

    February 23, 2026

    NAHCON Raises Alarm Over Fake Facebook Account Impersonating Chairman

    February 22, 2026
  • Picture Gallery
  • Opinion

    Nigeria Hajj Industry: Back To Square One – By Abubakar Jidda Usman

    February 11, 2026

    NAHCON Reconciliation Viewed as Positive Step for Hajj Administration – By Muhammad Sulaiman Gama

    February 2, 2026

    NAHCON Board’s Vote of No Confidence: A Mask for Self-Interest.

    February 1, 2026

    Nigeria Hajj Industry: When Would Pilgrims’ Interest Supercede Personal Interest of Handlers and Stakeholders

    January 31, 2026

    Who Is Afraid of Pakistan? By Faruku Umar

    January 31, 2026
  • Videos
  • HAUSA
HAJJ CHRONICLES
Home » Hajin 2026: Hukumar Alhazai Ta Jahar Kaduna Ta Kaddamar Da Bitar Maniyyata
Hausa

Hajin 2026: Hukumar Alhazai Ta Jahar Kaduna Ta Kaddamar Da Bitar Maniyyata

adminBy adminJanuary 7, 2026No Comments3 Mins Read
Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Email Telegram
FB IMG 1767783648682

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kaduna (KSPWA) ta kaddamar da shirin wayar da kai ga alhazai, wanda aka fi sani da BITA, domin shirye-shiryen aikin Hajjin shekarar 2026.

An sanarwar da Jami’in hulda da jama’a na Hukumar Ibrahim Datti Makarfi ya fitar, yace an gudanar da bikin kaddamar da shirin ne a ranar Asabar, 3 ga Janairu, 2026, a Cibiyar Karatun Al-Kur’ani ta Kinkinau, Jihar Kaduna.

Da yake jawabi a wajen taron, Shugaban Hukumar, Malam Salihu S. Abubakar, wanda Sakataren Gudanarwa, Malam Baba Rufa’i, ya wakilta, ya bayyana shirin BITA a matsayin muhimmin ginshiƙi a cikin shirye-shiryen aikin Hajjin Hukumar.

A cewarsa, an tsara shirin ne domin ilmantarwa, sanarwa, jagoranci da kuma shirya maniyyata ta fuskar addini, lafiya da kuma harkokin gudanarwa, domin tafiyar ibada zuwa Ƙasar Mai Tsarki.

Ya jaddada cewa jin daɗi da walwalar alhazan Jihar Kaduna shi ne babban abin da gwamnatin yanzu ta sa gaba, tare da tabbatar da cewa Hukumar ta kuduri aniyar samar da Hajji mai tsaro, jin daɗi da cikar ibada ga dukkan alhazai.

Ta hanyar shirin wayar da kai na BITA, za a ilmantar da maniyyata kan:
Dokoki da ibadojin Hajji
Matakan lafiya da tsaro
Dokoki da ƙa’idojin ƙasar Saudiyya
Ladabi, haƙuri da kyakkyawan ɗabi’a
Haɗin kai da zaman lafiya a tsakanin alhazai.

Shugaban ya bayyana cewa alhaji mai ilimi shi ne alhaji mai nasara, yana mai jaddada cewa shirin na da nufin kawar da ruɗani, rage kura-kurai, da tabbatar da bin ƙa’idoji yadda ya kamata.

Hukumar ta kuma bayyana ci gaban da ake samu a aikin sake inganta sansanin alhazan Jihar Kaduna  (Hajj Transit Camp) da ke Mando, a matsayin wani babban mataki na ƙara inganta jin daɗin alhazai.

Malam Salihu S. Abubakar ya tabbatar wa al’ummar Jihar Kaduna cewa aikin zai kammala kafin fara ayyukan Hajjin 2026.

Da zarar an kammala, ana sa ran sansanin zai kai matsayin zamani da ƙa’idojin ƙasa da ƙasa, tare da samar da:
Ingantattun masauki
Kyawawan wuraren tsafta
Ingantattun ayyukan lafiya da jin daɗi
Muhalli mai kyau, tsari da sauƙin gudanarwa
Ya ce wannan ci gaba na nuna ƙudurinsu na ci gaba da ɗaga matsayin jin daɗin alhazai da tsarin aikin Hajji a Jihar.

Shugaban ya yi amfani da damar wajen nuna godiya ta musamman ga Mai Girma Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, bisa goyon bayansa mai ɗorewa, hangen nesansa na ci gaba, da jajircewarsa wajen kula da walwalar alhazai.

Ya ce goyon bayan da Gwamnan ke bai wa Hukumar, musamman amincewa da tallafawa aikin sake inganta sansanin Hajji da sauran shirye-shiryen jin daɗi, na nuna salon jagorancinsa na tausayi da sanya jama’a a gaba.

A madadin Kwamitin Hajji na Musamman na Jihar Kaduna, shugabanci da ma’aikatan Hukumar, da kuma dukkan maniyyata, Shugaban ya nuna godiya ta zuciya ɗaya ga Gwamna bisa fifita mutunci, walwala da jin daɗin alhazan Jihar Kaduna.

Ya kuma yi kira ga dukkan maniyyata da su dauki shirin BITA da muhimmanci, su halarci dukkan zaman wayar da kai, su yi tambayoyi inda ya dace, tare da bin dukkan ƙa’idoji da umarnin da za a bayar.

Hukumar ta yaba wa malamai, masu gabatar da shiri, kafafen yaɗa labarai da sauran masu ruwa da tsaki bisa haɗin kai da goyon baya wajen tabbatar da aikin Hajji ba tare da tangarda ba.

.

Bitar Alhazai Hajin 2026 Hukumar Alhazai Ta Kaduna
Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp

Related Posts

NAHCON Ta Fayyace Batun Kujerun Hajjin 2026 da Ka’idojin Lafiya

February 24, 2026

Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Nemi Ƙarfafa Haɗin Gwiwa Da FAAN Da Kwastam Gabanin Ayyukan Hajji

February 16, 2026

Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Kaddamar Da Bitar Alhazai Ta Kafar Rediyo

February 15, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

Don't Miss
Nahcon

NAHCON Chairman Strengthens Ties with Saudi Embassy Ahead of 2026 Hajj

By adminFebruary 27, 20260

By Suwaiba Ahmad The Chairman/CEO of the National Hajj Commission of Nigeria (NAHCON), Ambassador Ismail…

Jigawa Pilgrims Board Seeks Smooth Immigration Process for 2026 Hajj

February 26, 2026

2026 Hajj: First Batch of Kano Pilgrims to Depart May 13

February 25, 2026

Hajj 2026: Sokoto Media Committee Urged to Ensure Smooth Information Flow

February 25, 2026
Stay In Touch
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • WhatsApp
Our Picks

NAHCON Chairman Strengthens Ties with Saudi Embassy Ahead of 2026 Hajj

February 27, 2026

Jigawa Pilgrims Board Seeks Smooth Immigration Process for 2026 Hajj

February 26, 2026

2026 Hajj: First Batch of Kano Pilgrims to Depart May 13

February 25, 2026

Hajj 2026: Sokoto Media Committee Urged to Ensure Smooth Information Flow

February 25, 2026
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
© 2026HAJJ CHRONILES

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.