Close Menu
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • Hajj News
  • Global
  • Health
  • Nahcon
  • Picture Gallery
  • Opinion
  • Videos
  • HAUSA
Facebook X (Twitter) Instagram
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram
SUBSCRIBE
  • Home
  • Hajj News

    2026/1447 Hajj Preparations Officially Launched as NAHCON Joins Global Pilgrimage Community in Closing Ceremony

    June 9, 2025

    No Lives Lost in Makkah Fire, Senate Foreign Affairs Committee Confirms

    June 9, 2025

    Pilgrimage and Leadership: How Governor Inuwa Yahaya Stood Tall Among His Peers During the 2025 Hajj – Abdulkadir Aliyu Shehu

    June 8, 2025

    From Crisis to Victory: NAHCON Chairman Called to Prostrate in Thanks for 2025 Hajj Breakthrough – By Shamwil Isah

    June 8, 2025

    Governor Abba Yusuf Disburses ₦361 Million Support to Kano Pilgrims in Mina

    June 8, 2025
  • Global

    Indonesia Plans to Acquire Land for Hajj Village Near Makkah’s Grand Mosque

    July 31, 2025

    Egypt To Halt Land Hajj Trips by 2026 Over Saudi Transport Policy Changes

    July 31, 2025

    UAE Unveils Streamlined Hajj 2026 Accreditation Process to Ensure Transparency and Quality

    July 24, 2025

    flyadeal Aims To Serve 75,000 International Hajj Pilgrims In 2025

    January 23, 2025

    Reflections on the 4th Hajj Conference and Exhibition in Jeddah – By Muhammad Ahmad Musa

    January 21, 2025
  • Health

    Gombe Muslim Pilgrim Board Commences Vaccination for 2025 Hajj Pilgrims – By Abdulqadir Aliyu Shehu

    April 28, 2025

    NAHCON Inaugurates Committee To Review National Medical Team Guidelines for Hajj 2025

    December 19, 2024

    Saudi Health Minister Strengthen Ties With Greece On Health Cooperation During Official Visit

    November 23, 2024

    Umm Al-Qura University volunteers extend help to pilgrims in Mina during Tashreeq

    June 17, 2024

    Hajj 2024: African pilgrim airlifted for emergency care

    June 14, 2024
  • Nahcon

    NAHCON, Private Tour Operators Hold Virtual Meeting to Streamline 2026 Hajj Operations – By Aminu Kabir

    October 8, 2025

    NAHCON Applauds President Tinubu, VP Shettima for Directive to Cut 2026 Hajj Cost

    October 7, 2025

    2026 Hajj: NAHCON Kicks Off Verification of Licensed Tour Operators – By Shafii Sani Mohammed

    October 6, 2025

    Pilgrims to Benefit as Tinubu, Shettima Secure Lower Hajj Costs – NAHCON Chairman

    October 2, 2025

    NAHCON Chairman Felicitates Nigerians on Independence Day

    October 1, 2025
  • Picture Gallery
  • Opinion

    Tinubu’s Hajj Fare Directive Aligns with NAHCON Chairman’s Vision for Affordable Pilgrimage – By Sirajo Salisu Jibia

    October 8, 2025

    Opinion: President Tinubu Is Right to Instruct NAHCON to Review and Cut Hajj Fares – By Muhammad Sulaiman Gama

    October 8, 2025

    Supporting NAHCON chairman’s leadership – By Raji Saidu Onipson

    September 17, 2025

    Hajj Pilgrimage and Misconception Over Funding – By Raheem Akingbolu

    August 27, 2025

    Prof. Abdullahi Saleh Usman: The Erudite Reformer Steering NAHCON Towards Excellence

    July 15, 2025
  • Videos
  • HAUSA
HAJJ CHRONICLES
Home » Hajin 2026: NAHCON ta fara aikin tantance Kamfanonin Jirgin Yawo – Daga Sani Shafi’i Mohammed
Hausa

Hajin 2026: NAHCON ta fara aikin tantance Kamfanonin Jirgin Yawo – Daga Sani Shafi’i Mohammed

adminBy adminOctober 6, 2025No Comments2 Mins Read
Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Email Telegram
IMG 20251006 165752

Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON) ta fara aikin tantancewa kamfanonin Jirgin yawo  masu zaman kansu, a matsayin wani ɓangare na shirye-shiryenta na gudanar da aikin Umrah da Hajj na shekarar 2026.

Aikin tantancewar ya biyo bayan ƙaddamar da kwamitin tantancewa da bayar da lasisin kamfanonin jirgin yawo masu zaman kansu da Shugaban Hukumar, Farfesa Abdullahi Saleh Usman, ya yi a makon da ya gabata a Abuja.

An bai wa kwamitin umarnin tantance da nazarin dukkan aikace-aikacen da kamfanoni masu neman lasisi ko sabunta lasisi suka gabatar, domin samun damar shiga cikin shirye-shiryen aikin Hajji na gaba.

An fara gudanar da aikin tantancewar a Jihar Kano, inda tawagar daga Sashen Kamfanonin Jirgin Yawo na Hukumar (Tour Operators Unit) ƙarƙashin sashen Ayyuka, Dubawa da Lasisi (OILS) ke jagoranta.

Tawagar tana ziyartar ofisoshin kamfanonin Jirgin Yawo don duba kayayyakin aikinsu, takardunsu, ma’aikatansu da kuma yadda suke bin ƙa’idojin aiki da Hukumar ta gindaya.

Yayin kaddamar da fara aikin, wani wakili na Hukumar ya bayyana cewa manufar tantancewar ita ce tabbatar da cewa kawai kamfanoni masu inganci, ƙwararru kuma masu ƙarfi a ɓangaren kuɗi ne za su samu lasisin gudanar da aikin Hajji da Umrah na shekarar 2026.

“Wannan tsarin yana da matuƙar muhimmanci wajen tabbatar da gaskiya, riƙon amana, da inganci. Yana tabbatar da cewa kawai waɗanda suka cika ƙa’idojin Hukumar da na hukumomin Saudiyya ne za su samu izinin gudanar da aiki,” in ji jami’in.

Farfesa Abdullahi Saleh Usman, yayin ƙaddamar da kwamitin a baya, ya jaddada cewa Hukumar za ta tsaya kai da fata wajen tabbatar da bin ƙa’ida, yana mai cewa sahihancin aikin Hajji da Umrah na Najeriya yana ta’allaka ne da inganci da gaskiyar kamfanonin balaguro masu lasisi.

Ana sa ran aikin tantancewar zai ci gaba zuwa sauran yankunan ƙasar nan a cikin ‘yan kwanaki masu zuwa, domin ya shafi dukkan kamfanonin balaguro masu rajista da masu neman sabunta rajista a fadin ƙasa.

Ta hanyar wannan aiki, NAHCON ta sake tabbatar da kudirinta na ƙarfafa tsari da kulawa, tare da tabbatar da cewa dukkan alhazai ‘yan Najeriya ko ta ofishin jihohi ko ta kamfanonin jirgin yawo masu zaman kansu sun sami ingantaccen hidima da kariya a lokacin gudanar da aikin Hajji da Umrah na shekarar 2026.

Hajin 2026 Kamfanonin Jirgin Yawo NAHCON Umrah
Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp

Related Posts

Umarnin Shugaba Tinubu Kan Rage Farashin Hajji Yayi Daidai Da Manufar Shugaban NAHCON Na Samar Da Arha Ga Maniyyata – Sirajo Salisu Jibia

October 8, 2025

NAHCON, Private Tour Operators Hold Virtual Meeting to Streamline 2026 Hajj Operations – By Aminu Kabir

October 8, 2025

Opinion: President Tinubu Is Right to Instruct NAHCON to Review and Cut Hajj Fares – By Muhammad Sulaiman Gama

October 8, 2025
Leave A Reply Cancel Reply

Don't Miss
Kano Pilgrims Board

FAAN Presents Award of Excellence to Kano Pilgrims Board DG

By adminOctober 9, 20250

The Federal Airports Authority of Nigeria (FAAN) has honoured the Director General of the Kano…

Umarnin Shugaba Tinubu Kan Rage Farashin Hajji Yayi Daidai Da Manufar Shugaban NAHCON Na Samar Da Arha Ga Maniyyata – Sirajo Salisu Jibia

October 8, 2025

Tinubu’s Hajj Fare Directive Aligns with NAHCON Chairman’s Vision for Affordable Pilgrimage – By Sirajo Salisu Jibia

October 8, 2025

NAHCON, Private Tour Operators Hold Virtual Meeting to Streamline 2026 Hajj Operations – By Aminu Kabir

October 8, 2025
Stay In Touch
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • WhatsApp
Our Picks

FAAN Presents Award of Excellence to Kano Pilgrims Board DG

October 9, 2025

Umarnin Shugaba Tinubu Kan Rage Farashin Hajji Yayi Daidai Da Manufar Shugaban NAHCON Na Samar Da Arha Ga Maniyyata – Sirajo Salisu Jibia

October 8, 2025

Tinubu’s Hajj Fare Directive Aligns with NAHCON Chairman’s Vision for Affordable Pilgrimage – By Sirajo Salisu Jibia

October 8, 2025

NAHCON, Private Tour Operators Hold Virtual Meeting to Streamline 2026 Hajj Operations – By Aminu Kabir

October 8, 2025
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
© 2025HAJJ CHRONILES

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.