Close Menu
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • Hajj News
  • Global
  • Health
  • Nahcon
  • Picture Gallery
  • Opinion
  • Videos
  • HAUSA
Facebook X (Twitter) Instagram
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram
SUBSCRIBE
  • Home
  • Hajj News

    2026/1447 Hajj Preparations Officially Launched as NAHCON Joins Global Pilgrimage Community in Closing Ceremony

    June 9, 2025

    No Lives Lost in Makkah Fire, Senate Foreign Affairs Committee Confirms

    June 9, 2025

    Pilgrimage and Leadership: How Governor Inuwa Yahaya Stood Tall Among His Peers During the 2025 Hajj – Abdulkadir Aliyu Shehu

    June 8, 2025

    From Crisis to Victory: NAHCON Chairman Called to Prostrate in Thanks for 2025 Hajj Breakthrough – By Shamwil Isah

    June 8, 2025

    Governor Abba Yusuf Disburses ₦361 Million Support to Kano Pilgrims in Mina

    June 8, 2025
  • Global

    Indonesia Plans to Acquire Land for Hajj Village Near Makkah’s Grand Mosque

    July 31, 2025

    Egypt To Halt Land Hajj Trips by 2026 Over Saudi Transport Policy Changes

    July 31, 2025

    UAE Unveils Streamlined Hajj 2026 Accreditation Process to Ensure Transparency and Quality

    July 24, 2025

    flyadeal Aims To Serve 75,000 International Hajj Pilgrims In 2025

    January 23, 2025

    Reflections on the 4th Hajj Conference and Exhibition in Jeddah – By Muhammad Ahmad Musa

    January 21, 2025
  • Health

    Gombe Muslim Pilgrim Board Commences Vaccination for 2025 Hajj Pilgrims – By Abdulqadir Aliyu Shehu

    April 28, 2025

    NAHCON Inaugurates Committee To Review National Medical Team Guidelines for Hajj 2025

    December 19, 2024

    Saudi Health Minister Strengthen Ties With Greece On Health Cooperation During Official Visit

    November 23, 2024

    Umm Al-Qura University volunteers extend help to pilgrims in Mina during Tashreeq

    June 17, 2024

    Hajj 2024: African pilgrim airlifted for emergency care

    June 14, 2024
  • Nahcon

    NAHCON Chairman Strengthens Ties with Saudi Embassy Ahead of 2026 Hajj

    February 27, 2026

    NAHCON Signs 2026 Hajj Airlift Agreement, Emphasizes Compliance and Efficiency

    February 25, 2026

    No Additional Slots for 2026 Hajj, Says NAHCON as Visa Issuance Nears

    February 24, 2026

    NAHCON Unveils Reforms, Clarifies Quota Adjustment Ahead of 2026 Hajj – By Abdulbasit Abba

    February 23, 2026

    NAHCON Raises Alarm Over Fake Facebook Account Impersonating Chairman

    February 22, 2026
  • Picture Gallery
  • Opinion

    Nigeria Hajj Industry: Back To Square One – By Abubakar Jidda Usman

    February 11, 2026

    NAHCON Reconciliation Viewed as Positive Step for Hajj Administration – By Muhammad Sulaiman Gama

    February 2, 2026

    NAHCON Board’s Vote of No Confidence: A Mask for Self-Interest.

    February 1, 2026

    Nigeria Hajj Industry: When Would Pilgrims’ Interest Supercede Personal Interest of Handlers and Stakeholders

    January 31, 2026

    Who Is Afraid of Pakistan? By Faruku Umar

    January 31, 2026
  • Videos
  • HAUSA
HAJJ CHRONICLES
Home » Hajin 2026: NAHCON ta fara aikin tantance Kamfanonin Jirgin Yawo – Daga Sani Shafi’i Mohammed
Hausa

Hajin 2026: NAHCON ta fara aikin tantance Kamfanonin Jirgin Yawo – Daga Sani Shafi’i Mohammed

adminBy adminOctober 6, 2025No Comments2 Mins Read
Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Email Telegram
IMG 20251006 165752

Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON) ta fara aikin tantancewa kamfanonin Jirgin yawo  masu zaman kansu, a matsayin wani ɓangare na shirye-shiryenta na gudanar da aikin Umrah da Hajj na shekarar 2026.

Aikin tantancewar ya biyo bayan ƙaddamar da kwamitin tantancewa da bayar da lasisin kamfanonin jirgin yawo masu zaman kansu da Shugaban Hukumar, Farfesa Abdullahi Saleh Usman, ya yi a makon da ya gabata a Abuja.

An bai wa kwamitin umarnin tantance da nazarin dukkan aikace-aikacen da kamfanoni masu neman lasisi ko sabunta lasisi suka gabatar, domin samun damar shiga cikin shirye-shiryen aikin Hajji na gaba.

An fara gudanar da aikin tantancewar a Jihar Kano, inda tawagar daga Sashen Kamfanonin Jirgin Yawo na Hukumar (Tour Operators Unit) ƙarƙashin sashen Ayyuka, Dubawa da Lasisi (OILS) ke jagoranta.

Tawagar tana ziyartar ofisoshin kamfanonin Jirgin Yawo don duba kayayyakin aikinsu, takardunsu, ma’aikatansu da kuma yadda suke bin ƙa’idojin aiki da Hukumar ta gindaya.

Yayin kaddamar da fara aikin, wani wakili na Hukumar ya bayyana cewa manufar tantancewar ita ce tabbatar da cewa kawai kamfanoni masu inganci, ƙwararru kuma masu ƙarfi a ɓangaren kuɗi ne za su samu lasisin gudanar da aikin Hajji da Umrah na shekarar 2026.

“Wannan tsarin yana da matuƙar muhimmanci wajen tabbatar da gaskiya, riƙon amana, da inganci. Yana tabbatar da cewa kawai waɗanda suka cika ƙa’idojin Hukumar da na hukumomin Saudiyya ne za su samu izinin gudanar da aiki,” in ji jami’in.

Farfesa Abdullahi Saleh Usman, yayin ƙaddamar da kwamitin a baya, ya jaddada cewa Hukumar za ta tsaya kai da fata wajen tabbatar da bin ƙa’ida, yana mai cewa sahihancin aikin Hajji da Umrah na Najeriya yana ta’allaka ne da inganci da gaskiyar kamfanonin balaguro masu lasisi.

Ana sa ran aikin tantancewar zai ci gaba zuwa sauran yankunan ƙasar nan a cikin ‘yan kwanaki masu zuwa, domin ya shafi dukkan kamfanonin balaguro masu rajista da masu neman sabunta rajista a fadin ƙasa.

Ta hanyar wannan aiki, NAHCON ta sake tabbatar da kudirinta na ƙarfafa tsari da kulawa, tare da tabbatar da cewa dukkan alhazai ‘yan Najeriya ko ta ofishin jihohi ko ta kamfanonin jirgin yawo masu zaman kansu sun sami ingantaccen hidima da kariya a lokacin gudanar da aikin Hajji da Umrah na shekarar 2026.

Hajin 2026 Kamfanonin Jirgin Yawo NAHCON Umrah
Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp

Related Posts

NAHCON Signs 2026 Hajj Airlift Agreement, Emphasizes Compliance and Efficiency

February 25, 2026

NAHCON Ta Fayyace Batun Kujerun Hajjin 2026 da Ka’idojin Lafiya

February 24, 2026

No Additional Slots for 2026 Hajj, Says NAHCON as Visa Issuance Nears

February 24, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

Don't Miss
Nahcon

NAHCON Chairman Strengthens Ties with Saudi Embassy Ahead of 2026 Hajj

By adminFebruary 27, 20260

By Suwaiba Ahmad The Chairman/CEO of the National Hajj Commission of Nigeria (NAHCON), Ambassador Ismail…

Jigawa Pilgrims Board Seeks Smooth Immigration Process for 2026 Hajj

February 26, 2026

2026 Hajj: First Batch of Kano Pilgrims to Depart May 13

February 25, 2026

Hajj 2026: Sokoto Media Committee Urged to Ensure Smooth Information Flow

February 25, 2026
Stay In Touch
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • WhatsApp
Our Picks

NAHCON Chairman Strengthens Ties with Saudi Embassy Ahead of 2026 Hajj

February 27, 2026

Jigawa Pilgrims Board Seeks Smooth Immigration Process for 2026 Hajj

February 26, 2026

2026 Hajj: First Batch of Kano Pilgrims to Depart May 13

February 25, 2026

Hajj 2026: Sokoto Media Committee Urged to Ensure Smooth Information Flow

February 25, 2026
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
© 2026HAJJ CHRONILES

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.