Close Menu
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • Hajj News
  • Global
  • Health
  • Nahcon
  • Picture Gallery
  • Opinion
  • Videos
  • HAUSA
Facebook X (Twitter) Instagram
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram
SUBSCRIBE
  • Home
  • Hajj News

    2026/1447 Hajj Preparations Officially Launched as NAHCON Joins Global Pilgrimage Community in Closing Ceremony

    June 9, 2025

    No Lives Lost in Makkah Fire, Senate Foreign Affairs Committee Confirms

    June 9, 2025

    Pilgrimage and Leadership: How Governor Inuwa Yahaya Stood Tall Among His Peers During the 2025 Hajj – Abdulkadir Aliyu Shehu

    June 8, 2025

    From Crisis to Victory: NAHCON Chairman Called to Prostrate in Thanks for 2025 Hajj Breakthrough – By Shamwil Isah

    June 8, 2025

    Governor Abba Yusuf Disburses ₦361 Million Support to Kano Pilgrims in Mina

    June 8, 2025
  • Global

    Indonesia Plans to Acquire Land for Hajj Village Near Makkah’s Grand Mosque

    July 31, 2025

    Egypt To Halt Land Hajj Trips by 2026 Over Saudi Transport Policy Changes

    July 31, 2025

    UAE Unveils Streamlined Hajj 2026 Accreditation Process to Ensure Transparency and Quality

    July 24, 2025

    flyadeal Aims To Serve 75,000 International Hajj Pilgrims In 2025

    January 23, 2025

    Reflections on the 4th Hajj Conference and Exhibition in Jeddah – By Muhammad Ahmad Musa

    January 21, 2025
  • Health

    Gombe Muslim Pilgrim Board Commences Vaccination for 2025 Hajj Pilgrims – By Abdulqadir Aliyu Shehu

    April 28, 2025

    NAHCON Inaugurates Committee To Review National Medical Team Guidelines for Hajj 2025

    December 19, 2024

    Saudi Health Minister Strengthen Ties With Greece On Health Cooperation During Official Visit

    November 23, 2024

    Umm Al-Qura University volunteers extend help to pilgrims in Mina during Tashreeq

    June 17, 2024

    Hajj 2024: African pilgrim airlifted for emergency care

    June 14, 2024
  • Nahcon

    Digital Transformation: NAHCON Teams Up with Alternative Bank for Hajj Savings Scheme”

    August 27, 2025

    NAHCON, Saudi Ministry of Hajj and Umrah Hold Virtual Meeting on 2026 Hajj Preparations

    August 25, 2025

    Prof. Abdullahi Saleh Usman Marks One Year at NAHCON After Successful 2025 Hajj – By Nura Ahmad Dakata

    August 23, 2025

    NAHCON to Stakeholders: No Extension of Saudi Deadlines for 2026 Hajj

    August 21, 2025

    Please Let NAHCON Be – By Fatima Sanda Usara

    August 21, 2025
  • Picture Gallery
  • Opinion

    Hajj Pilgrimage and Misconception Over Funding – By Raheem Akingbolu

    August 27, 2025

    Prof. Abdullahi Saleh Usman: The Erudite Reformer Steering NAHCON Towards Excellence

    July 15, 2025

    NAHCON: The Journey so Far, Under Professor Abdullahi Saleh Usman(Part 1)

    July 11, 2025

    Who’s Trying to Undermine NAHCON’s Progress?

    June 25, 2025

    Professor Abdullahi Saleh and Pilgrims Spiritual Reawakening – Dr Usman Ahmad Mustapha

    June 15, 2025
  • Videos
  • HAUSA
HAJJ CHRONICLES
Home » Hankalin Shugaban Hukumar NAHCON Bai Tashi Ba, Kuma Bai Girgiza Ba, Ya Himmatu Wajen Tabbatar Da Tsantsaini A Ayyukan Hajji – Daga Nura Ahmad Dakata 
Hausa

Hankalin Shugaban Hukumar NAHCON Bai Tashi Ba, Kuma Bai Girgiza Ba, Ya Himmatu Wajen Tabbatar Da Tsantsaini A Ayyukan Hajji – Daga Nura Ahmad Dakata 

adminBy adminFebruary 13, 2025No Comments4 Mins Read
Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Email Telegram
FB IMG 1739398212000

Yayin da ake kokarin bata masa suna a baya-bayan nan, Shugaban Hukumar Alhazai ta Najeriya (NAHCON), Farfesa Abdullahi Saleh Usman, ya ci gaba da jajircewa wajen ganin an tabbatar da gaskiya da rikon amana a ayyukan Hajji. 

 

Da yake mayar da martani game wani labara da wasu bata-gari ke yadawa da nufin bata sunan shugabancin NAHCO, Kodinetan kungiyar tallafawa alhazan Najeriya ta kafafen yada labarai na shiyyar Kano da Jigawa, Nura Ahmad, ya tabbatar da cewa “Babu wani batanci da zai sa shugaban hukumar NAHCON ya kauce daga babbar manufarsa ta tabbatar da gaskiya da rikon amana a ayyukan Hajji.”

 

A makonnin da suka gabata ne dai wasu zarge-zarge da ba su da tushe suka taso, inda aka yi karyar cewa Shugaban Hukumar NAHCON shi daya ya soke kwangilar da Hukumar ta yi da kamfanin dake yi wa alhazai hidima a Saudiyya, wanda hakan zai kawo cikas ga Alhazan Najeriyar a aikin Hajjin 2025.

 

Wannan ikirari dai mutane da yawa sun musanta shi daga hukumar NAHCON da masu ruwa da tsaki a aikin Hajji, wadanda suka tabbatar da cewa duk yarjejeniyoyin suna nan daram, kuma shirye-shiryen aikin hajjin na tafiya yadda ya kamata.

 

Farfesa Usman ya musanta wadannan tuhume-tuhume da kakkausar murya, musamman ikirarin da kungiyar shugabannin hukumomin jin dadin alhazai na jihohi suka yi kan cewa shi kadai ya soke kwangilar masu hidimar ba tare da tuntubarsu ba.

 

Ya kalubalanci wadanda ke wannan zargi da su bayar da kwararan hujjoji da za su tabbatar da ikirarin nasu, inda ya kara da cewa ba a yanke wani muhimmin hukunci dangane da ayyukan Hajji ba tare da tuntubar shugabannin kungiyar ba.

 

“Idan suna da wata hujja, to su gabatar da ita ga jama’a. NAHCON tana gudanar da aiki cikin gaskiya, kuma duk shawarar da aka yanke game da masu yi wa alhazai hidima an yi ne bisa bin ka’ida,” ya bayyana hakan a wata hira da ya yi da DCL Hausa.

 

Da yake karin haske kan ziyarar aikin da yake ci gaba da yi zuwa Saudiyya, Farfesa Usman ya bayyana cewa ya yi wata ganawa da ma’aikatansa na Makkah, inda suka yi masa bayani kan muhimman batutuwan da suka shafi shirye-shiryen Hajjin bana.

 

“Muna da wani taro da ma’aikatar Hajji da Umrah ta Saudiyya. Mun zo nan don fayyace batutuwa masu cin karo da juna dangane da masu ba da sabis. Ba za mu iya naɗe hannayenmu kawai mu ƙyale ƙoƙarinmu ya zama a banza ba,” Shugaban ya jaddada hakan

 

Shugaban ya kara da tabbatar wa alhazai da masu ruwa da tsaki cewa duk yarjejeniyoyin kwangilar suna nan daram sannan kuma shawarar da NAHCON ta yanke a koda yaushe yana da amfani ga alhazan Najeriya.

 

Ya ci gaba da cewa, “muna mayar da hankali ne kan ganin cewa alhazan Najeriya sun samu ingantattun hidimomi a farashi mai sauki. Ba za mu shagaltu da zarge-zargen da ba su da tushe balle makama ba.”

 

Masu kishin bunkasa walwalar alhazai da suka hada da Kungiyar ‘Yan jaridu masu Tallafawa Alhazan Najeriya (NHMST), sun yi kira ga al’umma da su yi watsi da wannan mummunan labari, suna masu bayyana hakan a matsayin wani yunkuri na masu zagon kasa na haifar da firgici na babu gaira ba dalili a cikin harkar Hajji.

 

“Wadannan labaran karya aikin wasu mutane ne da ke neman yin amfani da tsarin don biyan bukatun kansu,” in ji Kodinetan NHMST na kasa, Ibrahim Abubakar Nagarta, a wata sanarwa da ya fitar kwanan nan.

 

Duk da wannan kalubalen, NAHCON ta ci gaba da jajircewa wajen ganin an gudanar da aikin Hajji mai inganci ga alhazan Najeriya.

 

Hukumar karkashin jagorancin Farfesa Abdullahi Saleh Usman ta baiwa masu ruwa da tsaki tabbacin cewa za a ci gaba da yada bayanai kan aikin Hajjin 2025 ta hanyoyin da aka tabbatar.

 

A yayin da ake ci gaba da shirye-shiryen gudanar da aikin Hajin 2025, masu ruwa da tsaki sun bukaci hadin kai tare da mai da hankali kan hadafin hadin gwiwa na inganta ayyukan Hajjin Najeriya maimakon barin abubuwan da za su kawo cikas ga ci gabansa.

Farfesa Abdullahi Saleh Usman Hajj 2025 Shugaban NAHCON
Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp

Related Posts

Farfesa Abdullahi Sale Ya Cika Shekara 1 a NAHCON Bayan Nasarar Gudanar da Hajin 2025

August 24, 2025

Prof. Abdullahi Saleh Usman Marks One Year at NAHCON After Successful 2025 Hajj – By Nura Ahmad Dakata

August 23, 2025

Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Rage Kudin Haji Da Kashi 50 – Sheikh Tijjani Bala Kalarawi

August 21, 2025
Leave A Reply Cancel Reply

Don't Miss
Opinion

Hajj Pilgrimage and Misconception Over Funding – By Raheem Akingbolu

By adminAugust 27, 20250

There has been some unsavory focus on the National Hajj Commission of Nigeria (NAHCON) lately,…

Digital Transformation: NAHCON Teams Up with Alternative Bank for Hajj Savings Scheme”

August 27, 2025

NAHCON, Saudi Ministry of Hajj and Umrah Hold Virtual Meeting on 2026 Hajj Preparations

August 25, 2025

Farfesa Abdullahi Sale Ya Cika Shekara 1 a NAHCON Bayan Nasarar Gudanar da Hajin 2025

August 24, 2025
Stay In Touch
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • WhatsApp
Our Picks

Hajj Pilgrimage and Misconception Over Funding – By Raheem Akingbolu

August 27, 2025

Digital Transformation: NAHCON Teams Up with Alternative Bank for Hajj Savings Scheme”

August 27, 2025

NAHCON, Saudi Ministry of Hajj and Umrah Hold Virtual Meeting on 2026 Hajj Preparations

August 25, 2025

Farfesa Abdullahi Sale Ya Cika Shekara 1 a NAHCON Bayan Nasarar Gudanar da Hajin 2025

August 24, 2025
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
© 2025HAJJ CHRONILES

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.