Daga Abdulkadir Aliyu Shehu Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Gombe ta fara buga bizar mahajjatan da za su gudanar da aikin Hajjin shekarar 2026 .
Wannan mataki na daga cikin shirye-shiryen da hukumar ke yi domin tabbatar da cewa an kammala dukkanin muhimman abubuwan da suka shafi tafiyar mahajjatan jihar zuwa ƙasa mai tsarki.
Jami’an hukumar sun bayyana cewa fara buga bizar ya biyo bayan kammala tattara da kuma tantance takardun da mahajjata suka gabatar domin cika ka’idojin da ake bukata.
Sun ce wannan na daga cikin muhimman matakan da ake ɗauka domin tabbatar da cewa dukkan mahajjatan jihar sun cika sharuddan da hukumomin ƙasar Saudiyya suka gindaya.
Hukumar ta kuma bayyana cewa za a ci gaba da buga bizar ne a matakai daban-daban bisa ga yadda ake kammala tantance takardun mahajjatan.
Ta ce za a ci gaba da wannan aiki a kwanaki masu zuwa har sai an kammala buga bizar dukkan mahajjatan da suka cika ka’idojin tafiya daga jihar Gombe.
Jami’an hukumar sun tabbatar da cewa ana gudanar da aikin cikin tsari da gaskiya domin kauce wa duk wata matsala ko jinkiri da zai iya shafar tafiyar mahajjata.
Hukumar ta kuma bukaci mahajjatan da suka kammala biyan kudin kujerar Hajji da kuma gabatar da takardunsu su yi hakuri yayin da ake ci gaba da aikin.
Ta kara da cewa akwai wasu shirye-shirye da ake yi domin nasarar aikin Hajjin bana, ciki har da shirye-shiryen horas da mahajjata da kuma duba lafiyarsu.
A cewar hukumar, wadannan shirye-shirye na da matukar muhimmanci domin shirya mahajjata ta fuskar ibada, lafiya da kuma sanin yadda za su gudanar da aikin Hajji yadda ya kamata.
Haka kuma an shawarci mahajjata su kasance suna tuntubar hukumar domin samun sabbin bayanai game da ci gaban shirye-shiryen.
Hukumar ta ce za a sanar da mahajjata duk wani sabon mataki da zarar an samu cigaba a aikin buga bizar.
Ta jaddada kudurinta na ci gaba da samar da ingantattun ayyuka ga mahajjatan jihar tun daga shirye-shirye har zuwa lokacin da za su dawo daga aikin Hajji.
Hukumar ta kuma yi kira ga dukkan mahajjata da su ba da cikakken hadin kai ga jami’an da ke kula da wannan aiki domin samun nasarar shirye-shiryen.
Aikin Hajji na daga cikin rukunnan Musulunci guda biyar, wanda miliyoyin Musulmi daga sassa daban-daban na duniya ke gudanarwa a kowace shekara a biranen Makkah da Madina na ƙasar Saudiyya.

