Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Sakkwato tana sanar da fara wani tsari na musamman na wayar da kai da ilimantarwa a faɗin dukkanin ƙananan hukumomi 23 na jihar.
KARANTA LABARI MAKAMANCIN WANNAN : Hukumar Alhazai ta Sokoto ta Kammala Ɗora Bayanan Mahajjata 2,403 a Manhajar E-Track Masar
A sanarwar da shugaban sashen yada labarai da sadarwa na hukumar, Faruku Umar ya fitar, tace Shirin, wanda aka tsara domin shirya maniyyata aikin Hajjin shekarar 2026 yadda ya kamata, za a gudanar da shi ne ta haɗin gwiwa tsakanin Sashen Da’awah da Irshad na Hukumar tare da Kwamitin Malaman Wa’azi na Hajjin 2026 na jihar.
An tsara fara wannan shiri a ranar Alhamis, 7 ga Afrilu, 2026, inda zai ƙunshi muhimman fannoni na ibadun Hajji, ƙa’idoji, da kuma halayen da ake sa ran maniyyata su nuna yayin gudanar da aikin Hajji.
Ana sanar da dukkan maniyyata da cewa wajibi ne su halarci wannan shiri ba tare da gazawa ba, domin an tsara shi ne don basu ilimin da ya dace domin gudanar da ibadunsu yadda ya kamata, bisa koyarwar addinin Musulunci da kuma ƙa’idojin da aka shimfiɗa.
Hukumar na kira ga dukkan masu ruwa da tsaki da su bada cikakken haɗin kai tare da halartar wannan shiri domin samun nasarar gudanar da Hajji mai armashi da cike da lada.

