Close Menu
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • Hajj News
  • Global
  • Health
  • Nahcon
  • Picture Gallery
  • Opinion
  • Videos
  • HAUSA
Facebook X (Twitter) Instagram
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram
SUBSCRIBE
  • Home
  • Hajj News

    2026/1447 Hajj Preparations Officially Launched as NAHCON Joins Global Pilgrimage Community in Closing Ceremony

    June 9, 2025

    No Lives Lost in Makkah Fire, Senate Foreign Affairs Committee Confirms

    June 9, 2025

    Pilgrimage and Leadership: How Governor Inuwa Yahaya Stood Tall Among His Peers During the 2025 Hajj – Abdulkadir Aliyu Shehu

    June 8, 2025

    From Crisis to Victory: NAHCON Chairman Called to Prostrate in Thanks for 2025 Hajj Breakthrough – By Shamwil Isah

    June 8, 2025

    Governor Abba Yusuf Disburses ₦361 Million Support to Kano Pilgrims in Mina

    June 8, 2025
  • Global

    Indonesia Plans to Acquire Land for Hajj Village Near Makkah’s Grand Mosque

    July 31, 2025

    Egypt To Halt Land Hajj Trips by 2026 Over Saudi Transport Policy Changes

    July 31, 2025

    UAE Unveils Streamlined Hajj 2026 Accreditation Process to Ensure Transparency and Quality

    July 24, 2025

    flyadeal Aims To Serve 75,000 International Hajj Pilgrims In 2025

    January 23, 2025

    Reflections on the 4th Hajj Conference and Exhibition in Jeddah – By Muhammad Ahmad Musa

    January 21, 2025
  • Health

    Gombe Muslim Pilgrim Board Commences Vaccination for 2025 Hajj Pilgrims – By Abdulqadir Aliyu Shehu

    April 28, 2025

    NAHCON Inaugurates Committee To Review National Medical Team Guidelines for Hajj 2025

    December 19, 2024

    Saudi Health Minister Strengthen Ties With Greece On Health Cooperation During Official Visit

    November 23, 2024

    Umm Al-Qura University volunteers extend help to pilgrims in Mina during Tashreeq

    June 17, 2024

    Hajj 2024: African pilgrim airlifted for emergency care

    June 14, 2024
  • Nahcon

    NAHCON Approves Two 23kg Checked Bags for 2026 Hajj Pilgrims

    January 1, 2026

    NAHCON Begins Preparations for 2026 Hajj Medical Operations

    December 30, 2025

    No Contract Rollover: NAHCON Sets Record Straight on 2026 Hajj Procurement

    December 18, 2025

    The Penumbra of Influence: How Mercenary Journalism Built False Narratives Around NAHCON By Ahmad Mu’azu

    December 16, 2025

    NAHCON Opens Application Portal for 2026 National Medical Team

    December 12, 2025
  • Picture Gallery
  • Opinion

    The Need to Reintroduce Capacity-Building Workshops for Hajj Information Managers in Nigeria By Faruku Umar

    January 13, 2026

    Integrity, Discipline and Tireless Communication: Kano Pilgrims Board Shines Under Dedicated Leadership

    January 13, 2026

    NAHCON At 20: The Imperative of Repositioning Nigeria’s Hajj and Umrah Sector – Ibrahim Ishaq Jae

    January 12, 2026

    2026 Hajj Crisis: NAHCON, GACA Set to Clash Over Pilgrims’ Airlift

    January 11, 2026

    Man of the year: Professor Abdullahi Saleh, the game Changer – By Sagir Huguma

    January 3, 2026
  • Videos
  • HAUSA
HAJJ CHRONICLES
Home » Ku Yi Takatsantsan: NHMST ta gargadi masu kokarin kawo nakasu ga harkokin aikin Haji:
Hausa

Ku Yi Takatsantsan: NHMST ta gargadi masu kokarin kawo nakasu ga harkokin aikin Haji:

adminBy adminMarch 23, 2025Updated:March 23, 2025No Comments5 Mins Read
Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Email Telegram
file MeRxp68uF3NuTKZ1Xt26Kt

Daga: Ibrahim Abubakar Nagarta-NHMST

A baya-bayan nan ne kungiyar ‘yan jaridu dake tallafawa harkokin aikin Haji ta Najeriya ta sake cin karo da wani rade-radin rashin daidaito, son zuciya da kuma rahoton da ba ayi bincike a kan ba a kafafen yada labarai na wata jarida ta yanar gizo mai suna “Daily Nigerian” tana zargin shugabancin NAHCON da nuna son kai.

 

Idan dai za a iya tunawa, kusan watanni 2 da suka gabata, wani rahoto makamancin haka wanda ya kasance mai alaka da na baya-bayan nan, wani dandali na kafafen yada labarai na daban ya yada wa al’umma ba tare da sanin ya kamata ba, abin da ya banbanta shi ne cewa rahoton na baya-bayan nan an alakanta shi ne ga kungiyar manyan ma’aikatan gwamnati ta Najeriya, na NAHCON, duk da cewa kungiyar ta nesanta kanta da rahoton, duk da haka, rahotannin biyu sun ta’allaka ne kan manufa guda daya da suka hada da batanci da bata sunan shugabancin hukumar ta NAHCON a halin yanzu ta hanyar lakabi zarge-zarge marasa tushe na son zuciya, son zuciya da gazawa, a kan shugaban NAHCON Farfesa Abdullahi Sale Usman wanda ya jagoranci kawo gyara a harkokin aikin haji a idon musulmin Najeriya wanda tun tsawon shekaru ake ta neman samun irin wannan ci gaba.

 

Duk da haka jaridun guda biyu sun yi ikirarin cewa sun samo bayanan marasa tushe daga cikin hukumar musamman na baya-bayan nan, amma abin takaici masu bayar da wadannan rahotannin da ke cike da cece-kuce ba su taba yin amfani da salon jin ta daya bangaren ba a matsayin muhimman ka’ida na aikin jarida ba kamar yadda ka’idojin aikin suka bukata kafin su yi gaggawar sakin labarin.

 

Wannan dabi’a ta yi nuni da yadda suka yi aiki nesa-nesa da bin ka’idodi da doka da ake bi wajen gudanar da aikin jarida a matsayin wani fanni na kwararru.

 

Sai dai abin takaici, ko kuma aka yi sa’a, rahoton da kafafen yada labarai na baya-bayan nan da suka fitar ya zo ne a daidai lokacin da dimbin musulmin Najeriya masu kishin kasa ke bayyana farin ciki, da kwarin guiwa da kuma amincewa da salon jagorancin shugaban hukumar alhazai ta kasa, Farfesa Abdullahi Saleh Usman, ganin irin nasarorin da ba a taba samu ba a cikin kankanin lokaci na shugabancin hukumar.

 

Babban abin da ya fi daukar hankalin na nasarorin Farfesa Abdullahi Saleh Usman, shi ne irin tsauraran matakan da shugaban mai hangen nesa da tawagar ma’aikatansa masu himma suka dauka wajen kula da kudin aikin hajjin 2025, daga sama da abin da aka biya a shekarar da ta gabata, duk da sauyin da ake samu a kasuwar hada hadar kudaden kasashen waje, hakan ya samu ne ta hanyar hadin kai da shawarwari tare da masu ruwa da tsaki na hukumar ta NAHCON.

 

Gaskiya-Bincike Game da Sanya ‘yan Uwa Cikin Aiki:

 

Da farko dai rahoton da jaridara ‘Daily Nigeria’ suka fitar kwanan nan ba su da sahihanci da ma’auni gaba daya, musamman inda ta bayyana sunan wani Abdulmalik Diggi, a matsayin dan uwan shugaban NAHCON, kamar yadda binciken NHMST, ya nuna, Diggi ba ya da alaka ta jini da shugaban, sai dai kawai makusancinsa da amintacce ne na shugaban da Farfesa Abdullahi Saleh zai iya ba shi mukamin, wanda hakan ke nufin ya nada shi domin ya taimaka masa wajen samun nasarar aikin Haji

 

Hakazalika, inda jaridar “Daily Nigerian” ta yanar gizo ta sake ba da labarin cewa, ta tattaro wasu bayanai daga cikin hukumar kamar yadda ta saba cewa wai ana shirin kwashe ma’aikatan hukumar zuwa wasu ma’aikatu inda gungun ma’aikatan NAHCON zai shafa, duk da cewa jaridar ta kasa bayar da wata kwakkwarar hujjar da za ta iya tabbatar da hakan, amma kamar yadda ta saba ta yi amfani da wata Kalmar cewa daga cikin Hukumar a matsayin tushen labarinta

 

An san ’yan jarida a ko da yaushe da rashin tsoro da jajircewa kamar haka, marubucin wannan labarin kanzon kurege kuma mai cike da rudani, ya kamata ace ya bugi kirgi ya bayyana sunan su wadanda sika bas hi labarin da zummar sun nemi a sakaya sunayensu

 

A shawarce wannan tunani zai karawa jaridar samun Karin kwarin gwiwa da amincin jama’a wanda shine babban fatan kowace kafar labarai mai inganci.

 

A karshe, babbar tambayar da ‘yan Najeriya da dama ke yi a yanzu ita ce, shin a gaskiya wa ke da hannu a cikin rahoton da jaridar “Daily Nigerian” ta buga mai cike da rudani, tun bayan da kungiyar manyan ma’aikatan Najeriya na NAHCON ta musanta fitar da wani rahoto na wannan dabi’a kamar yadda ake danganta ta da shi? a yayin da ire-iren wadannan rahotanni marasa tushe ke ci gaba da fitowa a kafafen yada labarai ba tare da tuntubar wadanda ake zargi ba (na bangare na uku) ba kamar yadda ka’idojin aikin jarida suka bayyana, kungiyar ta Nigerian Hajj Media Support Team (NHMST), za ta kasance ba ta da wani zabi da ya wuce ta fara kama suna, ta hanyar fallasa wadanda suka dauki nauyin wadanda ake zargi da yin kiraye-kirayen domin jama’a su sansu, ba tare da la’akari da wadanda ba su da alaka da rubutaccen suna. don bata sunan Farfesa Abdullahi Saleh Usman, suna cikin ko wajen aikin hajji ko kuma musamman hukumar alhazai ta kasa.

Daily Nigerian NAHCON NHMST
Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp

Related Posts

Nagarta, Da’a da Sadarwa Cikin Jajircewa: Hukumar Alhazan Kano na Haskakawa ƙarƙashin Jagoranci Nagari

January 13, 2026

Rikicin Jigilar Alhazan 2026: Zargin Makircin Cikin Gida A NAHCON Na Barazana Ga Yarjejeniyar Sufurin Jirage Tsakanin Najeriya Da Saudia

January 12, 2026

Hajjin 2026: Jihar Gombe Ta Fara Gwajin Lafiya na Tilas ga Maniyyatan – Daga Abdulkadir Aliyu Shehu

January 12, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

Don't Miss
SPWA

Hajj 2026: Lagos begins medical screening for intending pilgrims, appoints LGA coordinators

By adminJanuary 14, 20260

The Lagos State Government has commenced medical screening for all intending pilgrims performing the 2026…

Hajj 2026: Kano Pilgrims Board Announces Deadline for Data Capturing

January 14, 2026

The Need to Reintroduce Capacity-Building Workshops for Hajj Information Managers in Nigeria By Faruku Umar

January 13, 2026

Nagarta, Da’a da Sadarwa Cikin Jajircewa: Hukumar Alhazan Kano na Haskakawa ƙarƙashin Jagoranci Nagari

January 13, 2026
Stay In Touch
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • WhatsApp
Our Picks

Hajj 2026: Lagos begins medical screening for intending pilgrims, appoints LGA coordinators

January 14, 2026

Hajj 2026: Kano Pilgrims Board Announces Deadline for Data Capturing

January 14, 2026

The Need to Reintroduce Capacity-Building Workshops for Hajj Information Managers in Nigeria By Faruku Umar

January 13, 2026

Nagarta, Da’a da Sadarwa Cikin Jajircewa: Hukumar Alhazan Kano na Haskakawa ƙarƙashin Jagoranci Nagari

January 13, 2026
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
© 2026HAJJ CHRONILES

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.