Close Menu
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • Hajj News
  • Global
  • Health
  • Nahcon
  • Picture Gallery
  • Opinion
  • Videos
  • HAUSA
Facebook X (Twitter) Instagram
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram
SUBSCRIBE
  • Home
  • Hajj News

    2026/1447 Hajj Preparations Officially Launched as NAHCON Joins Global Pilgrimage Community in Closing Ceremony

    June 9, 2025

    No Lives Lost in Makkah Fire, Senate Foreign Affairs Committee Confirms

    June 9, 2025

    Pilgrimage and Leadership: How Governor Inuwa Yahaya Stood Tall Among His Peers During the 2025 Hajj – Abdulkadir Aliyu Shehu

    June 8, 2025

    From Crisis to Victory: NAHCON Chairman Called to Prostrate in Thanks for 2025 Hajj Breakthrough – By Shamwil Isah

    June 8, 2025

    Governor Abba Yusuf Disburses ₦361 Million Support to Kano Pilgrims in Mina

    June 8, 2025
  • Global

    flyadeal Aims To Serve 75,000 International Hajj Pilgrims In 2025

    January 23, 2025

    Reflections on the 4th Hajj Conference and Exhibition in Jeddah – By Muhammad Ahmad Musa

    January 21, 2025

    Hajj and Umrah Expo 2025: Innovation and Collaboration Take Center Stage in Jeddah – By Fatima Sanda Usara

    January 14, 2025

    Makkah Red Crescent Boosts Preparedness to Heavy Rainfall

    January 6, 2025

    Intense Rainfall Sweeps Through Makkah, Madina and Jeddah

    January 6, 2025
  • Health

    Gombe Muslim Pilgrim Board Commences Vaccination for 2025 Hajj Pilgrims – By Abdulqadir Aliyu Shehu

    April 28, 2025

    NAHCON Inaugurates Committee To Review National Medical Team Guidelines for Hajj 2025

    December 19, 2024

    Saudi Health Minister Strengthen Ties With Greece On Health Cooperation During Official Visit

    November 23, 2024

    Umm Al-Qura University volunteers extend help to pilgrims in Mina during Tashreeq

    June 17, 2024

    Hajj 2024: African pilgrim airlifted for emergency care

    June 14, 2024
  • Nahcon

    NAHCON Chairman Attributes 2025 Hajj Success to Divine Blessings, Pledges Greater Efforts for 2026

    July 10, 2025

    The 2026 Hajj Countdown Has Begun: Why Early Compliance and Payment Is Crucial

    July 3, 2025

    NAHCON Concludes 2025 Hajj Return Operations as Last Flight Departs for Kaduna

    July 2, 2025

    Update on Nigeria’s 2025 Airlift

    July 1, 2025

    NAHCON Provides Update on Return Airlift, Cites July 2 as New Target Date

    June 26, 2025
  • Picture Gallery
  • Opinion

    NAHCON: The Journey so Far, Under Professor Abdullahi Saleh Usman(Part 1)

    July 11, 2025

    Who’s Trying to Undermine NAHCON’s Progress?

    June 25, 2025

    Professor Abdullahi Saleh and Pilgrims Spiritual Reawakening – Dr Usman Ahmad Mustapha

    June 15, 2025

    This is Ismail Shuaibu Musa — and this is his story – By Fatima Sanda Usara

    June 5, 2025

    Exposing Leadership Newspaper’s many lies against NAHCON chairman – By Ahmad Shafi’i PhD

    May 8, 2025
  • Videos
  • HAUSA
HAJJ CHRONICLES
Home » Ministan Lafiya Yayi Alkawarin Samar Da Goyon Baya Don Bunkasa Harkar Kula Da Lafiya Yayin Hajin 2025
Hausa

Ministan Lafiya Yayi Alkawarin Samar Da Goyon Baya Don Bunkasa Harkar Kula Da Lafiya Yayin Hajin 2025

adminBy adminMarch 25, 2025No Comments3 Mins Read
Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Email Telegram
1742857448674

Daga Muhammad Ahmad Musa

Ministan lafiya  na Najeriya, Farfesa Muhammad Ali Pate, ya kammala wata gagarumar ziyarar aiki zuwa cibiyoyin kula da lafiya na  hukumar kula da aikin Hajji ta kasa (NAHCON)  a birnin Makkah na kasar Saudiyya, lamarin da ke nuna cewa an samu sauyi a kokarin gwamnatin tarayya na bunkasa harkokin kiwon lafiyar alhazai.

Burin Shugaban Hukumar NAHCON Ya Cika, Bisa Rashin Samun Kari  A Kudin Kujerar Hajin 2025 – Daga Ibrahim Abubakar Nagarta

A ziyarar da ya kai ofishin hukumar NAHCON ta Ummul-Jud, Minista Pate ya ba da tabbacin goyon bayan gwamnati da nufin tunkarar kalubalen kiwon lafiya da alhazan Najeriya ke fuskanta yayin aikin Haji.

A Sanarwar da shugaban sashen hulda da jama’a na hukumar, Muhammad Ahmad Musa ya sanyawa hannu, yayin ziyarar ofishin hukumar dake Ummul Jud ,ta  nuna wani kuduri mai zurfi na gwamnatin tarayya, wanda ke nuna bayar da fifikon  jin dadin alhazai da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta yi.

“Aniyarmu  a bayyane yake,” in ji Minista Pate yayin tattaunawa da jami’an NAHCON.

“Idan aka yi la’akari da yanayin kiwon lafiya a duniya tun daga barkewar cutar sankarau da cutar shan inna, ya zama wajibi mu cika kuma mu wuce ka’idojin kiwon lafiya na Saudiyya. Tabbatar da sahihan takardun rigakafin, gami da katin gargadi ga dukkan mahajjatan Najeriya,wani abu ne da ya zama wajibi

Ministan Pate wanda ya samu rakiyar manyan wakilan ma’aikatar lafiya, ya gudanar da cikakken aikin duba motocin daukar marasa lafiya na NAHCON, da duba kayyakin da magunguna, da kuma tantance shirye-shiryen kayan aiki a asibitocin Najeriya da ke kasar Saudiyya.

Ziyarar ta bayyana wasu muhimman bangarori da ake bukatar ingantawa, da suka haɗa da haɓaka samar da muhimman magunguna, alluran rigakafi, na’urorin likitanci, da motocin daukar marasa lafiya masu aiki.

Shugaban Hukumar NAHCON, Farfesa Abdullahi Saleh Usman, ya yabawa shirin na Ministan, inda ya jaddada muhimmancinsa: “shigowarka cikin wannan tsari yayi nuni da yadda ake shirin sake inganta aikin kula da lafiyar alhazai Ganin yadda ‘yan Najeriya kusan 70,000 ke halarta a duk shekara, ziyarar  aikin da Ministan Pate ya yi ya nuna wani muhimmin ci gaba a cikin sa ido na gwamnati da tsare-tsare na kiwon lafiya.

Ya kuma yi tsokaci kan matsalolin da suka kunno kai, musamman yanayin zafi mai yawa a lokacin aikin Hajjin 2025 mai zuwa, tare da daukar matakan da suka dace don kiyaye lafiyar alhazai da walwala.

Wannan gagarumar ziyarar aiki i ta samar da ingantaccen hadin gwiwa tsakanin ma’aikatar lafiya ta Najeriya da NAHCON, tare da tabbatar da cewa mahajjatan Najeriya sun samu kulawa ta musamman a lokacin tafiyarsu ta Ibada

Hukumar NAHCON ta nanata sadaukarwar ta ga gaskiya, ba da hidima ta musamman da kuma ci gaba da inganta jin dadin alhazai.

Ministan lafiya da walwalar jama’a, Farfesa Mohammed Ali Pate ne ya gudanar da ziyarar, tare da rakiyar Shugaban Hukumar NAHCON, Farfesa Abdullahi Saleh Usman, Kwamishinan Ayyuka, PRSILS da PPMF, Prince Anofi’u Olanrewaju Elegusi, Farfesa Abubakar AbubakarYagawal; Prince Abdul-Razaq Aliyu, da kuma mamba mai wakiltar ma’aikatar lafiya ta tarayya Dr.Sa’edu Ahmad Dumbulwa.

Sauran wadanda suka halarci taron sun hada da Sakataren Hukumar Dokta Muhammad Mustapha Ali, Daraktoci, Mataimakan Daraktoci, da mataimakin Jami’in Hulda da Jama’a na Saudiyya Abubakar Lamin da sauran ma’aikatan Hukumar. 

Ali Pate Ministan lafiya NAHCON
Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp

Related Posts

NAHCON: The Journey so Far, Under Professor Abdullahi Saleh Usman(Part 1)

July 11, 2025

Shugaban NAHCON Ya Bukaci Gaggauta Rijistar Hajjin 2026, Ya Danganta Nasarar 2025 da Albarkar Ubangiji

July 11, 2025

Kidayar Lokacin Aikin Hajjin 2026 Ya Fara: Dalilin Da Yasa Cika Ka’idoji Da Biyan Kudin Hajji Tun Da Wuri Yake Da Muhimmanci – Daga Sani Muhammed Shafi’i

July 3, 2025
Leave A Reply Cancel Reply

Don't Miss
Opinion

NAHCON: The Journey so Far, Under Professor Abdullahi Saleh Usman(Part 1)

By adminJuly 11, 20250

By :Ibrahim Abubakar Nagarta In retrospect, the National hajj Commission of Nigeria (NAHCON) got…

Shugaban NAHCON Ya Bukaci Gaggauta Rijistar Hajjin 2026, Ya Danganta Nasarar 2025 da Albarkar Ubangiji

July 11, 2025

NAHCON Chairman Attributes 2025 Hajj Success to Divine Blessings, Pledges Greater Efforts for 2026

July 10, 2025

Mass Deportation: 8,000+ Illegal Migrants Sent Home from Saudi Arabia in Seven Days

July 8, 2025
Stay In Touch
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • WhatsApp
Our Picks

NAHCON: The Journey so Far, Under Professor Abdullahi Saleh Usman(Part 1)

July 11, 2025

Shugaban NAHCON Ya Bukaci Gaggauta Rijistar Hajjin 2026, Ya Danganta Nasarar 2025 da Albarkar Ubangiji

July 11, 2025

NAHCON Chairman Attributes 2025 Hajj Success to Divine Blessings, Pledges Greater Efforts for 2026

July 10, 2025

Mass Deportation: 8,000+ Illegal Migrants Sent Home from Saudi Arabia in Seven Days

July 8, 2025
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
© 2025HAJJ CHRONILES

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.