Close Menu
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • Hajj News
  • Global
  • Health
  • Nahcon
  • Picture Gallery
  • Opinion
  • Videos
  • HAUSA
Facebook X (Twitter) Instagram
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram
SUBSCRIBE
  • Home
  • Hajj News

    2026/1447 Hajj Preparations Officially Launched as NAHCON Joins Global Pilgrimage Community in Closing Ceremony

    June 9, 2025

    No Lives Lost in Makkah Fire, Senate Foreign Affairs Committee Confirms

    June 9, 2025

    Pilgrimage and Leadership: How Governor Inuwa Yahaya Stood Tall Among His Peers During the 2025 Hajj – Abdulkadir Aliyu Shehu

    June 8, 2025

    From Crisis to Victory: NAHCON Chairman Called to Prostrate in Thanks for 2025 Hajj Breakthrough – By Shamwil Isah

    June 8, 2025

    Governor Abba Yusuf Disburses ₦361 Million Support to Kano Pilgrims in Mina

    June 8, 2025
  • Global

    Indonesia Plans to Acquire Land for Hajj Village Near Makkah’s Grand Mosque

    July 31, 2025

    Egypt To Halt Land Hajj Trips by 2026 Over Saudi Transport Policy Changes

    July 31, 2025

    UAE Unveils Streamlined Hajj 2026 Accreditation Process to Ensure Transparency and Quality

    July 24, 2025

    flyadeal Aims To Serve 75,000 International Hajj Pilgrims In 2025

    January 23, 2025

    Reflections on the 4th Hajj Conference and Exhibition in Jeddah – By Muhammad Ahmad Musa

    January 21, 2025
  • Health

    Gombe Muslim Pilgrim Board Commences Vaccination for 2025 Hajj Pilgrims – By Abdulqadir Aliyu Shehu

    April 28, 2025

    NAHCON Inaugurates Committee To Review National Medical Team Guidelines for Hajj 2025

    December 19, 2024

    Saudi Health Minister Strengthen Ties With Greece On Health Cooperation During Official Visit

    November 23, 2024

    Umm Al-Qura University volunteers extend help to pilgrims in Mina during Tashreeq

    June 17, 2024

    Hajj 2024: African pilgrim airlifted for emergency care

    June 14, 2024
  • Nahcon

    NAHCON Chairman Strengthens Ties with Saudi Embassy Ahead of 2026 Hajj

    February 27, 2026

    NAHCON Signs 2026 Hajj Airlift Agreement, Emphasizes Compliance and Efficiency

    February 25, 2026

    No Additional Slots for 2026 Hajj, Says NAHCON as Visa Issuance Nears

    February 24, 2026

    NAHCON Unveils Reforms, Clarifies Quota Adjustment Ahead of 2026 Hajj – By Abdulbasit Abba

    February 23, 2026

    NAHCON Raises Alarm Over Fake Facebook Account Impersonating Chairman

    February 22, 2026
  • Picture Gallery
  • Opinion

    Nigeria Hajj Industry: Back To Square One – By Abubakar Jidda Usman

    February 11, 2026

    NAHCON Reconciliation Viewed as Positive Step for Hajj Administration – By Muhammad Sulaiman Gama

    February 2, 2026

    NAHCON Board’s Vote of No Confidence: A Mask for Self-Interest.

    February 1, 2026

    Nigeria Hajj Industry: When Would Pilgrims’ Interest Supercede Personal Interest of Handlers and Stakeholders

    January 31, 2026

    Who Is Afraid of Pakistan? By Faruku Umar

    January 31, 2026
  • Videos
  • HAUSA
HAJJ CHRONICLES
Home » Muhimman Nasarorin Hukumar NAHCON daga Hajjin 2025 zuwa Shirye-shiryen Hajjin 2026 – Daga Mohammed Ibn Mohd
Hausa

Muhimman Nasarorin Hukumar NAHCON daga Hajjin 2025 zuwa Shirye-shiryen Hajjin 2026 – Daga Mohammed Ibn Mohd

adminBy adminJanuary 2, 2026Updated:January 2, 2026No Comments4 Mins Read
Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Email Telegram
FB IMG 1749502554332

HAJJIN 2025: NAHCON ta ƙaddamar da kwamitin mutum 32 don soma aikin tankade da rairayar jiragen da za su yi aikin dakon Alhazai da kayansu

Hukumar Kula da Aikin Hajji ta Ƙasa (NAHCON) ƙarƙashin jagorancin Farfesa Abdullahi Saleh Usman ta nuna, cikin ɗan kankanin lokaci, cewa sauye-sauyen tsari na hukuma da aka gina bisa ƙwarewa da gaskiya na iya inganta ayyukan hidimar jama’a da alhazai matuƙa.

Zaman jagorancinsa ya nuna kwarewa da kuma sanin ya kamata sannan da nuna zuhudu don yi wa Najeriya da Alhazanta hidima ta yadda za a ayaba a koda yaushe.

Ɗaya daga cikin fitattun nasarorin NAHCON a ƙarƙashin Farfesa Usman shi ne dawo da tsari da ladabi a cikin shirye-shirye da aiwatar da aikin Hajji. Daga fara tuntuba da hukumomin Saudiyya tun da wuri zuwa bin jadawalin lokaci ba tare da sassauci ba, Hukumar ta rungumi salon aiki na gaba-gaba wanda ya rage rikice-rikicen aikin gaggawa.

Wannan sauyi ya haifar da ingantacciyar daidaituwa a fannin jigilar jiragen sama, masauki, abinci da sufuri ga Alhazan Najeriya fannonin da a baya suka jawo suka daga al’umma.

Haka kuma, an ba da muhimmanci sosai ga gaskiya. Jagorancin Farfesa Usman ya ƙarfafa tsarin kulawa na cikin gida tare da inganta haɗin gwiwa da hukumomin jin daɗin Alhazai na jihohi da kamfanonin yawon buɗe ido masu zaman kansu. Bayyanannun ƙa’idoji, tsauraran sharuddan bin doka, da buɗaɗɗun hanyoyin sadarwa sun rage rashin daidaito tare da ƙara amincewa tsakanin masu ruwa da tsaki. Ga Alhazai kuwa, hakan ya samar da fahimta mai kyau, da kuma ingantacciyar kulawa gaba ɗaya.

An kuma sake ba da kulawa ta musamman ga ka’idojin lafiya da tsaro. Ta hanyar tilasta bin ƙa’idojin lafiya na Saudiyya da ƙarfafa gwaje-gwajen lafiya kafin tafiya, NAHCON ta ɗauki matakai masu muhimmanci wajen kare Alhazai da kuma martabar Najeriya a matsayin ƙasa mai ɗaukar nauyin aika Alhazai cikin tsari. Waɗannan matakai, ko da yake wani lokaci ba su jawo farin jini ba, sun nuna jagoranci mai fifita martaba da amincewa na dogon lokaci fiye da sauƙin ayi gaggawa na ɗan lokaci.

Bayan harkokin aiki kawai, Farfesa Usman ya sake mayar da NAHCON a matsayin hukuma mai daraja a fagen diflomasiyyar Hajji ta duniya. Ingantacciyar alaƙa da hukumomin Hajji na Saudiyya da masu samar da ayyuka ta ƙarfafa matsayar Najeriya wajen tattaunawa, tare da tabbatar da kyakkyawan rabon dama da ingancin ayyuka ga Alhazan Najeriya.

A taƙaice, nasarar NAHCON a ƙarƙashin Farfesa Abdullahi Usman ba ta tsaya ga sauƙaƙa gudanar da aikin Hajji kaɗai ba, illa kafa tsare-tsare, ƙa’idoji, da al’adun sauyi na gyara. Duk da cewa har yanzu akwai ƙalubale, yanayin da ake ciki yana nuna cewa harkokin Hajji na Najeriya na tafiya ne ta hanyar dorewa, ƙwarewa, da mayar da hankali ga jin daɗin Alhazai, samun nasara da ta cancanci yabo da ƙarfafawa.

Haka kuma, sashen Yaɗa Labarai da dab’i na NAHCON ya cancanci yabo saboda ƙwarewar da sashen ke nunawa, inda ya taka muhimmiyar rawa wajen irin ma’aikatan da ke wannan sashe a ƙarƙashin jagorancin Fatima Sanda Usara, ya yi fice wajen tsayuwar daka, bayyana gaskiya, da daidaito a harkar gudanar da bayanai.

Salon aikinta na ƙwarewa mai natsuwa sannan kuma cike da sanin makamshin aiki, musamman a lokutan da jama’a ke neman bayanai akai akai, Ta jagoranci wannan sashe wajen fede biri tun daga kai har wutsi wajen bayyana gaskiya domin al’umma su san abinda ake ciki.

Sannan kuma akwai Mohammed Musa Danbaba, wanda rawar da yake takawa ta daidaita bayanai ta taimaka wajen tsarawa da sauƙaƙa yadda bayanai ke gudana a cikin gida, tare da daidaita saƙonni tsakanin sassa daban-daban domin tabbatar da fahimta ɗaya da inganci a sadarwar jama’a.

Gudummawar Ahmed Mu’azu, Mataimaki na musamman ga Shugaban Hukumar kan Harkokin Watsa Labarai, ta ƙara ƙarfafa wannan tsari ta hanyar bayar da goyon bayan dabarun kafafen yaɗa labarai da kuma tabbatar da cewa manufofin Shugaban Hukumar da fifikon ayyukan NAHCON suna fitowa fili.

Ma’aikata irin su Suwaiba Ahmad, Sani Shafi’i, da wasu da dama a cikin sashen na taimakawa manema labarai, musamman domin sanin abinda ake kullawa a hukumar da kuma inda ake warwarewa.

Mohammed Ibn Mohd, Marubuci ne mazaunin Abuja, Najeriya.

(PT Hausa)

Farfesa Abdullahi Saleh Usman Hajj 2025 Hajj 2026 NAHCON
Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp

Related Posts

NAHCON Chairman Strengthens Ties with Saudi Embassy Ahead of 2026 Hajj

February 27, 2026

Jigawa Pilgrims Board Seeks Smooth Immigration Process for 2026 Hajj

February 26, 2026

2026 Hajj: First Batch of Kano Pilgrims to Depart May 13

February 25, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

Don't Miss
Nahcon

NAHCON Chairman Strengthens Ties with Saudi Embassy Ahead of 2026 Hajj

By adminFebruary 27, 20260

By Suwaiba Ahmad The Chairman/CEO of the National Hajj Commission of Nigeria (NAHCON), Ambassador Ismail…

Jigawa Pilgrims Board Seeks Smooth Immigration Process for 2026 Hajj

February 26, 2026

2026 Hajj: First Batch of Kano Pilgrims to Depart May 13

February 25, 2026

Hajj 2026: Sokoto Media Committee Urged to Ensure Smooth Information Flow

February 25, 2026
Stay In Touch
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • WhatsApp
Our Picks

NAHCON Chairman Strengthens Ties with Saudi Embassy Ahead of 2026 Hajj

February 27, 2026

Jigawa Pilgrims Board Seeks Smooth Immigration Process for 2026 Hajj

February 26, 2026

2026 Hajj: First Batch of Kano Pilgrims to Depart May 13

February 25, 2026

Hajj 2026: Sokoto Media Committee Urged to Ensure Smooth Information Flow

February 25, 2026
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
© 2026HAJJ CHRONILES

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.