Close Menu
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • Hajj News
  • Global
  • Health
  • Nahcon
  • Picture Gallery
  • Opinion
  • Videos
  • HAUSA
Facebook X (Twitter) Instagram
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram
SUBSCRIBE
  • Home
  • Hajj News

    2026/1447 Hajj Preparations Officially Launched as NAHCON Joins Global Pilgrimage Community in Closing Ceremony

    June 9, 2025

    No Lives Lost in Makkah Fire, Senate Foreign Affairs Committee Confirms

    June 9, 2025

    Pilgrimage and Leadership: How Governor Inuwa Yahaya Stood Tall Among His Peers During the 2025 Hajj – Abdulkadir Aliyu Shehu

    June 8, 2025

    From Crisis to Victory: NAHCON Chairman Called to Prostrate in Thanks for 2025 Hajj Breakthrough – By Shamwil Isah

    June 8, 2025

    Governor Abba Yusuf Disburses ₦361 Million Support to Kano Pilgrims in Mina

    June 8, 2025
  • Global

    Indonesia Plans to Acquire Land for Hajj Village Near Makkah’s Grand Mosque

    July 31, 2025

    Egypt To Halt Land Hajj Trips by 2026 Over Saudi Transport Policy Changes

    July 31, 2025

    UAE Unveils Streamlined Hajj 2026 Accreditation Process to Ensure Transparency and Quality

    July 24, 2025

    flyadeal Aims To Serve 75,000 International Hajj Pilgrims In 2025

    January 23, 2025

    Reflections on the 4th Hajj Conference and Exhibition in Jeddah – By Muhammad Ahmad Musa

    January 21, 2025
  • Health

    Gombe Muslim Pilgrim Board Commences Vaccination for 2025 Hajj Pilgrims – By Abdulqadir Aliyu Shehu

    April 28, 2025

    NAHCON Inaugurates Committee To Review National Medical Team Guidelines for Hajj 2025

    December 19, 2024

    Saudi Health Minister Strengthen Ties With Greece On Health Cooperation During Official Visit

    November 23, 2024

    Umm Al-Qura University volunteers extend help to pilgrims in Mina during Tashreeq

    June 17, 2024

    Hajj 2024: African pilgrim airlifted for emergency care

    June 14, 2024
  • Nahcon

    NAHCON Directs Airlines to Issue 2026 Hajj Tickets Ahead of Departure

    December 4, 2025

    Hajj Chronicles Uncovers Alleged Internal Sabotage Plot Targeting NAHCON Leadership

    December 3, 2025

    NAHCON Strengthens Hajj Savings Scheme, Signs MoU with Four Islamic Banks

    December 1, 2025

    NAHCON Chairman Mourns the Passing Sheikh Dahiru Bauchi

    November 28, 2025

    NAHCON Boosts Preparations for 2026 Hajj, Targets Zero Complaints in Madina

    November 27, 2025
  • Picture Gallery
  • Opinion

    Are 44,000 Pilgrims Really Due Refunds? A Deep Dive into IHR’s Hajj 2025 Report

    December 9, 2025

    AFGSAN Backs Call to Return NAHCON to SGF’s Office

    December 7, 2025

    Muslim Coalition Urges Tinubu to Review NAHCON and Return Its Supervision to the SGF

    December 5, 2025

    When Journalism Becomes a Weapon; And Why NAHCON’s Chairman Must Be Defended

    November 24, 2025

    Fact-Check Analysis: Newspoint News Misrepresented NAHCON Chairman’s Interviews – The Real Facts Behind The Claims

    October 30, 2025
  • Videos
  • HAUSA
HAJJ CHRONICLES
Home » NAHCON Ta Umurci Kamfanonin Jiragen Sama Su Fara Fitar da Tikitin 2026 Hajj Kafin Tashi
Hausa

NAHCON Ta Umurci Kamfanonin Jiragen Sama Su Fara Fitar da Tikitin 2026 Hajj Kafin Tashi

adminBy adminDecember 4, 2025Updated:December 4, 2025No Comments4 Mins Read
Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Email Telegram
FB IMG 1764857128770

Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON) ta umurci dukkan kamfanonin daukar mahajjata na 2026 tare da hadin gwiwar Hukumomin Jin Dadin Alhazai na Jihohi da su fara fitar da tikitin jirgi ga dukkan mahajjatan da za su tashi domin gudanar da ibadar Hajj ta 2026.

A sanarwar da Mataimakiyar Daraktar yada labarai da hulda da jama’a, Fatima Sanda Usara ta sanayawa hannu, tace wannan umarni ya fito ne yau 4 ga Disamba 2026, a wani taro da NAHCON ta gudanar tare da hukumomin alhazai na jihohi da kamfanonin jiragen 2026 a hedikwatar hukumar da ke Abuja.

Umarnin na nufin tabbatar da cewa kowane mahajjaci ya san takamaiman jadawalin tashinsa wanda ya hada da kwanan wata, lokaci da filin jirgin da zai tashi. Hakan zai taimaka wajen rage matsalolin kuskuren bayanan kafin saukar alhazai da ake turawa Saudiyya, wanda ke janyo tsaiko wajen rabon katin Nusuk da sauran shirye-shiryen aiki.

A fara Hajj na 2026, duk mahajjacin da ya rasa jirgi zai fuskanci hukunci mai tsanani. Wannan saboda an haɗa tikitin kowane mahajjaci kai tsaye da katin Nusuk, wanda za a ajiye shi a cikin motocin da aka ware musu a Saudiyya, wadanda za su kaisu otel dinsu.

Saboda haka, bayan fitowar visa, ba zai kara yiwuwa ga mahajjaci ya canza rukuni ba; za su zauna cikin kungiyoyin da aka samar da musu visa. Kowace rukuni na mutum 45 za su tafi tare, su zauna tare a Makkah, Madinah da Masha’ir, sannan su dawo tare zuwa Najeriya bayan kammala Hajj.

Haka kuma, dole ne NAHCON ta shigar da bayanan kafin saukar alhazai a dandalin Nusuk Masar awanni 72 kafin tashin kowanne jirgi. Bayanannin sun hada da lambar rukuni, sunayen alhazan rukuni, bayanan masauki, ginin da aka ware, da lambar gadon kwana. Duk mahajjacin da bai bayyana a filin jirgi ba a lokacin da aka tsara, za a dauke shi a matsayin wanda bai zo ba kuma zai biya tarar da ta shafi kujerar da bai yi amfani da ita ba. Wannan hukunci zai shafi duk wani bangare da ya yi sakaci.

Haka nan, Ma’aikatar Hajj da Umrah ta Saudiyya ta gabatar da sabon katin shiga jirgi da za a raba wa kowane mahajjaci kafin tashi. Katin zai ƙunshi muhimman bayanai irin su: sunan kamfanin jirgi, yawan kujeru, sunan jiha, sunayen mahajjata a cikin jirgin, filin tashin jirgi, lokaci, filin sauka da lokacin zuwan jirgi.

Mai taimakawa shugaban NAHCON kan al’amura na musammam, Dr. Danbaba Haruna, ya bayyana cewa hukumar ta kammala yin ajiyar sansani da sauran ayyuka. Sai dai idan adadin ajiyar bai dace da aikin masauki da Saudiyya ta tanada ba, za a mayar da kudaden da suka wuce a asusun NAHCON, kuma hakan na nufin an rasa guraben. Ya ja hankalin Hukumar Alhazai ta Jihohi da su gaggauta tura kudaden Hajj domin kauce wa rasa karin gurabe.

NAHCON ta kara jaddada cewa sabon sharadin lafiya da Saudiyya ta kafa dole ne a bi shi sosai domin akwai hukunci ga masu karya doka.

Ma’aikatar Hajj da Umrah ta ce duk mahajjacin da aka samu da daya daga cikin cututtukan da ke hana tafiya, ba zai yi Hajj ba, kuma zai biya kudin korarsa idan ya tafi. An umurci hukumomin alhazai na jihohi da su yi aiki ne kawai da cibiyoyin lafiya masu inganci da aka tantance wajen bayar da takardar shaidar lafiya. Cutar da ke hana zuwa Hajj sun hada da: gazawar manyan sassan jiki (zuciya, hanta, koda, da huhu), marasa lafiya masu karbar chemotherapy ko radiotherapy, cututtukan hauka ko lalacewar kwakwalwa da ke rage natsuwa, mantuwa mai tsanani, ciki mai hadari a kowane mataki, da cututtuka masu yaduwa.

A wani bangare, an riga an aika rabon jiragen 2026 ga kowace Hukumar Alhazai ta Jihar tare da shawarar su yi hadin gwiwa. Sai dai rabon na iya canzawa saboda binciken fasaha da na kayan aiki. Kamfanonin jirgin 2026 sune: Air Peace, FlyNas, Max Air da Umza Air.

Shugaban NAHCON, Farfesa Abdullahi Saleh Usman, ya jaddada bukatar hadin kai tsakanin hukumomin alhazai na jihohi, kamfanonin jirgi da hukumar NAHCON, yana mai cewa nasarar NAHCON nasarar kowa ce.

2026 Hajj kamfanonin Jirgin Sama NAHCON Tikitin Jirgi
Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp

Related Posts

Hajj 2026: Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Rufe Karbar Kudi Bayan Karewar Wa’adin Da NAHCON Ta Bayar

December 9, 2025

AFGSAN Backs Call to Return NAHCON to SGF’s Office

December 7, 2025

Muslim Coalition Urges Tinubu to Review NAHCON and Return Its Supervision to the SGF

December 5, 2025
Leave A Reply Cancel Reply

Don't Miss
Hausa

Hajj 2026: Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Rufe Karbar Kudi Bayan Karewar Wa’adin Da NAHCON Ta Bayar

By adminDecember 9, 20250

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kano ta sanar da cewa ta kammala karɓar kuɗin…

Are 44,000 Pilgrims Really Due Refunds? A Deep Dive into IHR’s Hajj 2025 Report

December 9, 2025

AFGSAN Backs Call to Return NAHCON to SGF’s Office

December 7, 2025

Muslim Coalition Urges Tinubu to Review NAHCON and Return Its Supervision to the SGF

December 5, 2025
Stay In Touch
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • WhatsApp
Our Picks

Hajj 2026: Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Rufe Karbar Kudi Bayan Karewar Wa’adin Da NAHCON Ta Bayar

December 9, 2025

Are 44,000 Pilgrims Really Due Refunds? A Deep Dive into IHR’s Hajj 2025 Report

December 9, 2025

AFGSAN Backs Call to Return NAHCON to SGF’s Office

December 7, 2025

Muslim Coalition Urges Tinubu to Review NAHCON and Return Its Supervision to the SGF

December 5, 2025
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
© 2025HAJJ CHRONILES

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.