Close Menu
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • Hajj News
  • Global
  • Health
  • Nahcon
  • Picture Gallery
  • Opinion
  • Videos
  • HAUSA
Facebook X (Twitter) Instagram
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram
SUBSCRIBE
  • Home
  • Hajj News

    2026/1447 Hajj Preparations Officially Launched as NAHCON Joins Global Pilgrimage Community in Closing Ceremony

    June 9, 2025

    No Lives Lost in Makkah Fire, Senate Foreign Affairs Committee Confirms

    June 9, 2025

    Pilgrimage and Leadership: How Governor Inuwa Yahaya Stood Tall Among His Peers During the 2025 Hajj – Abdulkadir Aliyu Shehu

    June 8, 2025

    From Crisis to Victory: NAHCON Chairman Called to Prostrate in Thanks for 2025 Hajj Breakthrough – By Shamwil Isah

    June 8, 2025

    Governor Abba Yusuf Disburses ₦361 Million Support to Kano Pilgrims in Mina

    June 8, 2025
  • Global

    Indonesia Plans to Acquire Land for Hajj Village Near Makkah’s Grand Mosque

    July 31, 2025

    Egypt To Halt Land Hajj Trips by 2026 Over Saudi Transport Policy Changes

    July 31, 2025

    UAE Unveils Streamlined Hajj 2026 Accreditation Process to Ensure Transparency and Quality

    July 24, 2025

    flyadeal Aims To Serve 75,000 International Hajj Pilgrims In 2025

    January 23, 2025

    Reflections on the 4th Hajj Conference and Exhibition in Jeddah – By Muhammad Ahmad Musa

    January 21, 2025
  • Health

    Gombe Muslim Pilgrim Board Commences Vaccination for 2025 Hajj Pilgrims – By Abdulqadir Aliyu Shehu

    April 28, 2025

    NAHCON Inaugurates Committee To Review National Medical Team Guidelines for Hajj 2025

    December 19, 2024

    Saudi Health Minister Strengthen Ties With Greece On Health Cooperation During Official Visit

    November 23, 2024

    Umm Al-Qura University volunteers extend help to pilgrims in Mina during Tashreeq

    June 17, 2024

    Hajj 2024: African pilgrim airlifted for emergency care

    June 14, 2024
  • Nahcon

    NAHCON Chairman Strengthens Ties with Saudi Embassy Ahead of 2026 Hajj

    February 27, 2026

    NAHCON Signs 2026 Hajj Airlift Agreement, Emphasizes Compliance and Efficiency

    February 25, 2026

    No Additional Slots for 2026 Hajj, Says NAHCON as Visa Issuance Nears

    February 24, 2026

    NAHCON Unveils Reforms, Clarifies Quota Adjustment Ahead of 2026 Hajj – By Abdulbasit Abba

    February 23, 2026

    NAHCON Raises Alarm Over Fake Facebook Account Impersonating Chairman

    February 22, 2026
  • Picture Gallery
  • Opinion

    Nigeria Hajj Industry: Back To Square One – By Abubakar Jidda Usman

    February 11, 2026

    NAHCON Reconciliation Viewed as Positive Step for Hajj Administration – By Muhammad Sulaiman Gama

    February 2, 2026

    NAHCON Board’s Vote of No Confidence: A Mask for Self-Interest.

    February 1, 2026

    Nigeria Hajj Industry: When Would Pilgrims’ Interest Supercede Personal Interest of Handlers and Stakeholders

    January 31, 2026

    Who Is Afraid of Pakistan? By Faruku Umar

    January 31, 2026
  • Videos
  • HAUSA
HAJJ CHRONICLES
Home » Rikicin Jigilar Alhazan 2026: Zargin Makircin Cikin Gida A NAHCON Na Barazana Ga Yarjejeniyar Sufurin Jirage Tsakanin Najeriya Da Saudia
Hausa

Rikicin Jigilar Alhazan 2026: Zargin Makircin Cikin Gida A NAHCON Na Barazana Ga Yarjejeniyar Sufurin Jirage Tsakanin Najeriya Da Saudia

adminBy adminJanuary 12, 2026Updated:January 12, 2026No Comments3 Mins Read
Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Email Telegram
FB IMG 1766066402041

Daga Abubakar Idi Maru, Abuja Shirye-shiryen aikin Hajjin 2026 na Nijeriya na fuskantar babbar barazana, sakamakon ƙara taɓarɓarewar dangantaka tsakanin Hukumar Kula da Aikin Hajji ta Ƙasa (NAHCON) da Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Sama ta Masarautar Saudiyya (GACA).

Rahotanni na nuni da cewa hukumomin sufurin jiragen saman Saudiyya na tunanin ɗaukar matakan hukunci, ciki har da yiwuwar hana jiragen Nijeriya samun izinin sauka, bisa zargin cewa Nijeriya ta kasa bin ka’idojin Yarjejeniyar Sufurin Jiragen Sama ta Ƙasashe Biyu (BASA) da aka cimma a 2015.

A cikin rikicin akwai gazawar NAHCON wajen tura cikakken jadawalin tashin jiragen Hajji ga GACA, wanda yake zama wajibi kafin a ba da izinin sauka da wucewa ta sararin samaniya a lokacin aikin Hajji.

Masana harkar jiragen sama na gargaɗin cewa ci gaba da jinkirta aika wannan jadawali na iya jefa Nijeriya cikin matakin hukunci daga Saudiyya, tare da haifar da babbar matsala ga dukkan tsarin jigilar alhazai.

Bincike ya nuna cewa rabon jihohi da jiragen sama da NAHCON ta fitar a watan Disambar 2025 bai yi la’akari da ragin yawan alhazai daga jihohin da aka bai wa kamfanin jirgin Saudiyya Flynas ba, yayin da aka ƙara wa jiragen Nijeriya kaso mai yawa. Maimakon a daidaita adadin domin cika sharadin rabon kashi 50–50 na BASA tare da fitar da jadawalin jirage mai inganci, ana zargin Hukumar ta bar wannan rashin daidaito ya ci gaba, lamarin da ya ƙara rikitar da tsarin shirye-shiryen GACA.

Wasu manyan majiyoyi a cikin NAHCON na zargin cewa lamarin ya wuce sakaci ko rashin ƙwarewa, suna danganta shi da ganganci da mugun nufi daga Kwamishinan Ayyuka na Hukumar, Prince Anofiu Elegushi. A cewar waɗannan majiyoyi, an yi watsi da matakan gyara da gangan duk da sanin cewa rashin amincewar jadawalin jirage na iya bai wa hukumomin Saudiyya damar takaita ko ma dakatar da jigilar alhazan Nijeriya, abin da zai cutar da walwalar alhazai da martabar Gwamnatin Tarayya a idon duniya.

Rikicin ya ƙara tsananta ne da ikirarin cewa wani tsohon mataimaki mai ritaya na ci gaba da tsoma baki a harkokin jiragen sama ba tare da wata doka ko izini ba.

Masana harkar sufurin jiragen sama na gargaɗin cewa wannan haɗakar tsoma bakin ciki, tangardar tsarin gudanarwa da rashin bin ƙa’idoji na iya sake tayar da rikicin da aka warware tun 2015, inda suka tunatar da cewa Nijeriya na cikin ƙasashe kaɗan da Saudiyya ta bai wa sassauci wajen aiwatar da BASA a hankali wata dama da ba a bai wa ƙasashe da dama masu aikin Hajji ba.

Da yake rahotanni ke nuna cewa hukumomin Saudiyya sun fara gajiya, masu ruwa da tsaki na jaddada cewa duk wani matakin hukunci da za a ɗauka zai fi shafar alhazan Nijeriya ta fuskar jinkirin jirage, rage kujeru ko ma hana shiga filayen jiragen saman Saudiyya a lokacin kololuwar aikin Hajji.

A sakamakon haka, ana kira da a gaggauta sa bakin Gwamnatin Tarayya, a hanzarta tura jadawalin jiragen Hajji da ya dace da BASA zuwa GACA, tare da gudanar da bincike a bayyane kan zargin ganganci na ciki, domin kauce wa rikicin da ka iya zama babbar matsala ta ƙasa, ta diflomasiyya da ta jinƙai.

Abubakar Idi Maru,
Ɗan jarida mai bincike,
Abuja.

GACA Hajj 2026 Makircin Cikin Gida Najeriya Saudi
Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp

Related Posts

NAHCON Chairman Strengthens Ties with Saudi Embassy Ahead of 2026 Hajj

February 27, 2026

Jigawa Pilgrims Board Seeks Smooth Immigration Process for 2026 Hajj

February 26, 2026

2026 Hajj: First Batch of Kano Pilgrims to Depart May 13

February 25, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

Don't Miss
Nahcon

NAHCON Chairman Strengthens Ties with Saudi Embassy Ahead of 2026 Hajj

By adminFebruary 27, 20260

By Suwaiba Ahmad The Chairman/CEO of the National Hajj Commission of Nigeria (NAHCON), Ambassador Ismail…

Jigawa Pilgrims Board Seeks Smooth Immigration Process for 2026 Hajj

February 26, 2026

2026 Hajj: First Batch of Kano Pilgrims to Depart May 13

February 25, 2026

Hajj 2026: Sokoto Media Committee Urged to Ensure Smooth Information Flow

February 25, 2026
Stay In Touch
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • WhatsApp
Our Picks

NAHCON Chairman Strengthens Ties with Saudi Embassy Ahead of 2026 Hajj

February 27, 2026

Jigawa Pilgrims Board Seeks Smooth Immigration Process for 2026 Hajj

February 26, 2026

2026 Hajj: First Batch of Kano Pilgrims to Depart May 13

February 25, 2026

Hajj 2026: Sokoto Media Committee Urged to Ensure Smooth Information Flow

February 25, 2026
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
© 2026HAJJ CHRONILES

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.