Close Menu
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • Hajj News
  • Global
  • Health
  • Nahcon
  • Picture Gallery
  • Opinion
  • Videos
  • HAUSA
Facebook X (Twitter) Instagram
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram
SUBSCRIBE
  • Home
  • Hajj News

    2026/1447 Hajj Preparations Officially Launched as NAHCON Joins Global Pilgrimage Community in Closing Ceremony

    June 9, 2025

    No Lives Lost in Makkah Fire, Senate Foreign Affairs Committee Confirms

    June 9, 2025

    Pilgrimage and Leadership: How Governor Inuwa Yahaya Stood Tall Among His Peers During the 2025 Hajj – Abdulkadir Aliyu Shehu

    June 8, 2025

    From Crisis to Victory: NAHCON Chairman Called to Prostrate in Thanks for 2025 Hajj Breakthrough – By Shamwil Isah

    June 8, 2025

    Governor Abba Yusuf Disburses ₦361 Million Support to Kano Pilgrims in Mina

    June 8, 2025
  • Global

    Indonesia Plans to Acquire Land for Hajj Village Near Makkah’s Grand Mosque

    July 31, 2025

    Egypt To Halt Land Hajj Trips by 2026 Over Saudi Transport Policy Changes

    July 31, 2025

    UAE Unveils Streamlined Hajj 2026 Accreditation Process to Ensure Transparency and Quality

    July 24, 2025

    flyadeal Aims To Serve 75,000 International Hajj Pilgrims In 2025

    January 23, 2025

    Reflections on the 4th Hajj Conference and Exhibition in Jeddah – By Muhammad Ahmad Musa

    January 21, 2025
  • Health

    Gombe Muslim Pilgrim Board Commences Vaccination for 2025 Hajj Pilgrims – By Abdulqadir Aliyu Shehu

    April 28, 2025

    NAHCON Inaugurates Committee To Review National Medical Team Guidelines for Hajj 2025

    December 19, 2024

    Saudi Health Minister Strengthen Ties With Greece On Health Cooperation During Official Visit

    November 23, 2024

    Umm Al-Qura University volunteers extend help to pilgrims in Mina during Tashreeq

    June 17, 2024

    Hajj 2024: African pilgrim airlifted for emergency care

    June 14, 2024
  • Nahcon

    NAHCON Chairman Strengthens Ties with Saudi Embassy Ahead of 2026 Hajj

    February 27, 2026

    NAHCON Signs 2026 Hajj Airlift Agreement, Emphasizes Compliance and Efficiency

    February 25, 2026

    No Additional Slots for 2026 Hajj, Says NAHCON as Visa Issuance Nears

    February 24, 2026

    NAHCON Unveils Reforms, Clarifies Quota Adjustment Ahead of 2026 Hajj – By Abdulbasit Abba

    February 23, 2026

    NAHCON Raises Alarm Over Fake Facebook Account Impersonating Chairman

    February 22, 2026
  • Picture Gallery
  • Opinion

    Nigeria Hajj Industry: Back To Square One – By Abubakar Jidda Usman

    February 11, 2026

    NAHCON Reconciliation Viewed as Positive Step for Hajj Administration – By Muhammad Sulaiman Gama

    February 2, 2026

    NAHCON Board’s Vote of No Confidence: A Mask for Self-Interest.

    February 1, 2026

    Nigeria Hajj Industry: When Would Pilgrims’ Interest Supercede Personal Interest of Handlers and Stakeholders

    January 31, 2026

    Who Is Afraid of Pakistan? By Faruku Umar

    January 31, 2026
  • Videos
  • HAUSA
HAJJ CHRONICLES
Home » Umarnin Shugaba Tinubu Kan Rage Farashin Hajji Yayi Daidai Da Manufar Shugaban NAHCON Na Samar Da Arha Ga Maniyyata – Sirajo Salisu Jibia
Hausa

Umarnin Shugaba Tinubu Kan Rage Farashin Hajji Yayi Daidai Da Manufar Shugaban NAHCON Na Samar Da Arha Ga Maniyyata – Sirajo Salisu Jibia

adminBy adminOctober 8, 2025No Comments4 Mins Read
Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Email Telegram
IMG 20250928 WA0010

Umarnin da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya bayar kwanan nan ga Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON) da ta gaggauta sake duba farashin kujerar Hajjin shekarar 2026 tare da rage shi, wani babban ci gaba ne da ya dace da manufar Shugaban Hukumar, Farfesa Abdullahi Saleh Usman, wanda burinsa tun farko shi ne tabbatar da cewa aikin Hajji ya kasance mai araha ga dukkan Musulman Najeriya.

Umarnin Shugaban Kasa ya bukaci NAHCON da ta sake lissafa farashin kujerun Hajji domin ya nuna yadda Naira ta samu karuwa a kan Dala.

Wannan mataki na gwamnati ya zo a kan gaba, yana ceton maniyyatan Najeriya daga tsadar kujerar da aka sanar da ita tun farko, wadda aka kirga bisa “hasashen sauyin kudi na N1,550 a kan Dala daya. Farashin farko ya kasance tsakanin N8.1m zuwa N8.5m bisa ga yankuna daban-daban.

Ana sa ran sabon umarnin zai rage farashin zuwa kusan tsakanin N7.6m da N7.7m.

Murnar da Shugaban NAHCON ya nuna kan wannan labari abin fahimta ne, domin ya tabbatar da jajircewarsa wajen rage farashi da kula da walwalar maniyyata.

Tun daga lokacin da ya hau Shugabancin hukumar, Farfesa Saleh Usman ya sanya araha da ingantacciyar hidima ga maniyyata a matsayin babban ginshikin aikinsa.

Ko da yake sabon yinkurin rage farashin ya samo asali ne daga karfin Naira, ya ginu ne kan matakan rage kudi da shugabancin NAHCON ya riga ya dauka tun da farko.

Daya daga cikin manyan nasarorin da shugabancin ya cimma shi ne tanadin rangwame ga maniyyata ta hanyar samun saukin farashin hidima da ya kai kimanin Naira biliyan 19 gaba daya. An cimma hakan ne bayan samun rangwamen fiye da N200,000 kan kowane maniyyaci daga wurin masu yin hidima ga Alhazai a Saudiyya, abin da ya zama babban tanadi ga kusan maniyyata 66,000 da aka warewa Najeriya.

Wani babban abin alfahari kuma shi ne yadda NAHCON ta inganta tsarin kwangiloli, wanda ya taka rawar gani wajen nasarar aikin Hajjin 2025.

A wancan lokacin, tawagar Farfesa Saleh Usman ta yi gyara kan kwangilolin ayyuka domin su dace da adadin maniyyatan da aka yi rajista, mataki wanda ya hana asarar kudi da yawa kuma ya taimaka wajen rage farashin kujerar.

NAHCON kuma ta fadada tsarin Hajj Savings Scheme, inda shugaban ya kara karfafa tsarin ta hanyar hada kai da karin bankuna domin karfafa al’adar ajiya tun da wuri, don rage wahalar biyan kudi da lokaci daya.

Sai dai duk wadannan nasarori ba su samu ba tare da kalubale ba. Kudurinsa na samar da hidimomi masu inganci da araha ya taba shiga rikici da wasu masu muradun kansu.

Rahotanni na nuna cewa tsadar da aka bayyana a farko na iya da nasaba da matsin lamba daga wasu bangarori da ke da hannu a harkar kwangila, musamman batun zaben kamfani daya tilo da zai rika gudanar da ayyukan din Hajji.

Manufar Farfesa Saleh Usman tun farko ita ce a dauki kamfanoni da dama masu inganci domin gudanar da ayyuka, domin hakan zai haifar da gasa mai kyau wadda za ta rage kudi kuma ta inganta sabis ga maniyyata. Saboda haka, wannan umarnin Shugaban Kasa ya zama tamkar karfafa guiwa da kuma damar da za ta bashi damar kaucewa duk wata cikas ta son kai ko na birokrasiya wajen cimma manufar rage farashi bisa mafi kyawun canjin kudi.

Domin cika wannan buri, Shugaban NAHCON yana kokarin karfafa al’adar biyan kudi da wuri. Ya bukaci Jihohin da ke da Hukumar Jin Dadin Alhazai su tabbatar da cewa suna aika kudin maniyyata cikin lokaci.

Wannan yana da matukar muhimmanci domin hakan zai bai wa Babban Bankin Kasa (CBN) damar sayen kudin kasashen waje bisa farashin da ya inganta, wanda hakan zai tabbatar da ajiye kudi ga maniyyata.

An sanya ranar karshe ta biyan kaso 50% na kudin Hajji a ranar 8 ga Oktoba, 2025, yayin da cikakken biyan kudin zai kare a ranar 31 ga Disamba, 2025.

A fili yake cewa Farfesa Abdullahi Saleh Usman yana kan hanya madaidaiciya wajen gudanar da daya daga cikin ayyukan Hajji mafi nasara da araha a tarihin Najeriya. Jajircewarsa kan amfani da kudi cikin hikima tare da goyon bayan fadar Shugaban Kasa na nuna alamar cewa aikin Hajjin 2026 zai kasance mai tarihi wanda zai tabbatar da manufar samun sauki da ingantaccen sabis ga maniyyata.

Sirajo Salisu Jibia
Ya rubuta daga Japan.

Kudin Haji Shugaba Tinubu Shugaban NAHCON
Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp

Related Posts

NAHCON Ta Fayyace Batun Kujerun Hajjin 2026 da Ka’idojin Lafiya

February 24, 2026

Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Nemi Ƙarfafa Haɗin Gwiwa Da FAAN Da Kwastam Gabanin Ayyukan Hajji

February 16, 2026

Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Kaddamar Da Bitar Alhazai Ta Kafar Rediyo

February 15, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

Don't Miss
Nahcon

NAHCON Chairman Strengthens Ties with Saudi Embassy Ahead of 2026 Hajj

By adminFebruary 27, 20260

By Suwaiba Ahmad The Chairman/CEO of the National Hajj Commission of Nigeria (NAHCON), Ambassador Ismail…

Jigawa Pilgrims Board Seeks Smooth Immigration Process for 2026 Hajj

February 26, 2026

2026 Hajj: First Batch of Kano Pilgrims to Depart May 13

February 25, 2026

Hajj 2026: Sokoto Media Committee Urged to Ensure Smooth Information Flow

February 25, 2026
Stay In Touch
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • WhatsApp
Our Picks

NAHCON Chairman Strengthens Ties with Saudi Embassy Ahead of 2026 Hajj

February 27, 2026

Jigawa Pilgrims Board Seeks Smooth Immigration Process for 2026 Hajj

February 26, 2026

2026 Hajj: First Batch of Kano Pilgrims to Depart May 13

February 25, 2026

Hajj 2026: Sokoto Media Committee Urged to Ensure Smooth Information Flow

February 25, 2026
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
© 2026HAJJ CHRONILES

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.