Close Menu
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • Hajj News
  • Global
  • Health
  • Nahcon
  • Picture Gallery
  • Opinion
  • Videos
  • HAUSA
Facebook X (Twitter) Instagram
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram
SUBSCRIBE
  • Home
  • Hajj News

    2026/1447 Hajj Preparations Officially Launched as NAHCON Joins Global Pilgrimage Community in Closing Ceremony

    June 9, 2025

    No Lives Lost in Makkah Fire, Senate Foreign Affairs Committee Confirms

    June 9, 2025

    Pilgrimage and Leadership: How Governor Inuwa Yahaya Stood Tall Among His Peers During the 2025 Hajj – Abdulkadir Aliyu Shehu

    June 8, 2025

    From Crisis to Victory: NAHCON Chairman Called to Prostrate in Thanks for 2025 Hajj Breakthrough – By Shamwil Isah

    June 8, 2025

    Governor Abba Yusuf Disburses ₦361 Million Support to Kano Pilgrims in Mina

    June 8, 2025
  • Global

    Indonesia Plans to Acquire Land for Hajj Village Near Makkah’s Grand Mosque

    July 31, 2025

    Egypt To Halt Land Hajj Trips by 2026 Over Saudi Transport Policy Changes

    July 31, 2025

    UAE Unveils Streamlined Hajj 2026 Accreditation Process to Ensure Transparency and Quality

    July 24, 2025

    flyadeal Aims To Serve 75,000 International Hajj Pilgrims In 2025

    January 23, 2025

    Reflections on the 4th Hajj Conference and Exhibition in Jeddah – By Muhammad Ahmad Musa

    January 21, 2025
  • Health

    Gombe Muslim Pilgrim Board Commences Vaccination for 2025 Hajj Pilgrims – By Abdulqadir Aliyu Shehu

    April 28, 2025

    NAHCON Inaugurates Committee To Review National Medical Team Guidelines for Hajj 2025

    December 19, 2024

    Saudi Health Minister Strengthen Ties With Greece On Health Cooperation During Official Visit

    November 23, 2024

    Umm Al-Qura University volunteers extend help to pilgrims in Mina during Tashreeq

    June 17, 2024

    Hajj 2024: African pilgrim airlifted for emergency care

    June 14, 2024
  • Nahcon

    NAHCON Chairman Strengthens Ties with Saudi Embassy Ahead of 2026 Hajj

    February 27, 2026

    NAHCON Signs 2026 Hajj Airlift Agreement, Emphasizes Compliance and Efficiency

    February 25, 2026

    No Additional Slots for 2026 Hajj, Says NAHCON as Visa Issuance Nears

    February 24, 2026

    NAHCON Unveils Reforms, Clarifies Quota Adjustment Ahead of 2026 Hajj – By Abdulbasit Abba

    February 23, 2026

    NAHCON Raises Alarm Over Fake Facebook Account Impersonating Chairman

    February 22, 2026
  • Picture Gallery
  • Opinion

    Nigeria Hajj Industry: Back To Square One – By Abubakar Jidda Usman

    February 11, 2026

    NAHCON Reconciliation Viewed as Positive Step for Hajj Administration – By Muhammad Sulaiman Gama

    February 2, 2026

    NAHCON Board’s Vote of No Confidence: A Mask for Self-Interest.

    February 1, 2026

    Nigeria Hajj Industry: When Would Pilgrims’ Interest Supercede Personal Interest of Handlers and Stakeholders

    January 31, 2026

    Who Is Afraid of Pakistan? By Faruku Umar

    January 31, 2026
  • Videos
  • HAUSA
HAJJ CHRONICLES
Home » Hajji 2025: Kungiyar Fararen Hula Ta Yi Kira Ga Gwamnoni Su Mayar Da Hankali Kan Fayil Din Harkokin Hajji
Hausa

Hajji 2025: Kungiyar Fararen Hula Ta Yi Kira Ga Gwamnoni Su Mayar Da Hankali Kan Fayil Din Harkokin Hajji

adminBy adminOctober 23, 2024No Comments3 Mins Read
Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Email Telegram
news6710a19b07f6a
news6710a19b07f6a

Dangane da jinkirin wajen sanar da fara rijistar maniyyata da wasu hukumomin jin dadin Alhazai na Jihohi da suke yi, kungiyar masu bayar da rahotanni da sa ido kan harkokin Hajji da Umrah ta Najeriya mai zaman kanta,ta yi kira ga Gwamnonin Jihohin da su baiwa al’amuran Hajji fifiko a Jihohinsu.

 

“Ya zuwa lokacin rubuta wannan labari, Jihohin Neja, Sokoto da Borno har yanzu ba su fara aikin rajistar ba duk da cewa sun samu umarnin Hukumar Alhazai ta Najeriya (NAHCON) a watan Agusta na cewa Jihohin su fara rajista.

 

“Muna sane da cewa har yanzu wasu Sakatarorin zartarwa na Hukumar Jin Dadin Alhazai Musulmi ba su mika rahoton aikin Hajjin 2024 ga Gwamnoninsu ba, wanda a sakamakon haka har yanzu ba su samu amincewar fara rajistar maniyyata daga shugabanninsu ba,” in ji IHR. a wata sanarwa mai dauke da sa hannun kodinetan ta na kasa, Ibrahim Mohammed, ranar Laraba.

 

Kungiyar ta fararen hula ta kuma nuna damuwarta kan yadda har yanzu ba a fara rijistar wasu jihohi ba ko da ana sa ran za su mika kaso na farko na kudaden ajiyar maniyyata zuwa hukumar NAHCON, tun daga ranar 2 ga watan Oktoba (kamar yadda kalandar hukumar NAHCON ta 2025 ta nuna) don isarwa ga kamfanonin don biyan kudin tantina a Mina.

 

“Cewa Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jiha za ta bukaci wata amincewa ta daban daga Gwamnonin Jihohi don fara rajistar maniyyata ko da bayan an ba su izini daga hukumar kula da aikin hajji, wani shiri ne na musamman na hadin gwiwa ga masana’antar Hajji wanda ke bukatar mafita cikin gaggawa”.

 

Kungiyar ta ce “Ya zama dole a lura cewa a ranar 23 ga watan Oktoba ma’aikatar aikin Hajji ta Saudiyya ta fara raba tanti ga kasashen da suea halartar aikin Hajji da suka biya.

 

 

 

“Duk wani sakataren zartarwa na Hukumar Jin Dadin Alhazai Musulmai na Jiha wanda bai gabatar da rahoton aikin Hajjin na 2024 watanni hudu bayan aikin Hajjin 2024 ba to a cire shi tare da maye gurbinsa da wanda ya cancanta,” in ji kungiyar.

 

Sannan kuma ya tunatar da gwamnonin jihohin cewa jinkirin fara rajistar maniyyata da Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihohi ke yi, shi ne ummul haba’isin matsalar rashin hidima da alhazan Najeriya ke fuskanta duk shekara a Saudiyya.

 

“Yin ragistar a makare yana haifar da jinkirin tura asusun rijistar maniyyata zuwa NAHCON, wanda hakan ya shafi gazawar hukumar wajen biyan kudade ga kamfanoni dake yin hidima ga alhazai da ke Saudiyya a daidai lokacin da zasu bad a damar yin isassun shirye-shirye don samar da ingantacciyar hidima ga maniyyatanmu.

 

“Ma’aikatan gudanarwa na jihohi na kawo cikas sosai wajen aiwatar da kalandar Hajji, don haka akwai bukatar a yi wani abu don yin daidai da dokar kafa hukumar NAHCON ta shekarar 2006, don baiwa maniyyatan jihohi damar fara rajista da wuri ba tare da jiran amincewar shugabannin zartarwa na jiha ba.

 

“Aikin Hajji al’amari ne na duniya wanda ake sa ran sama da kasashe 162 da ke halartar taron za su aiwatar a lokaci daya da aka fitar duk shekara kamar yadda ma’aikatar aikin Hajji ta Saudiyya ta fitar don zama taswirar jagora don shirye-shiryen aikin Hajji,” in ji kungiyar

Hajj 2025 IHR NAHCON Ragistar Aikin Haji
Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp

Related Posts

NAHCON Signs 2026 Hajj Airlift Agreement, Emphasizes Compliance and Efficiency

February 25, 2026

NAHCON Ta Fayyace Batun Kujerun Hajjin 2026 da Ka’idojin Lafiya

February 24, 2026

No Additional Slots for 2026 Hajj, Says NAHCON as Visa Issuance Nears

February 24, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

Don't Miss
Nahcon

NAHCON Chairman Strengthens Ties with Saudi Embassy Ahead of 2026 Hajj

By adminFebruary 27, 20260

By Suwaiba Ahmad The Chairman/CEO of the National Hajj Commission of Nigeria (NAHCON), Ambassador Ismail…

Jigawa Pilgrims Board Seeks Smooth Immigration Process for 2026 Hajj

February 26, 2026

2026 Hajj: First Batch of Kano Pilgrims to Depart May 13

February 25, 2026

Hajj 2026: Sokoto Media Committee Urged to Ensure Smooth Information Flow

February 25, 2026
Stay In Touch
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • WhatsApp
Our Picks

NAHCON Chairman Strengthens Ties with Saudi Embassy Ahead of 2026 Hajj

February 27, 2026

Jigawa Pilgrims Board Seeks Smooth Immigration Process for 2026 Hajj

February 26, 2026

2026 Hajj: First Batch of Kano Pilgrims to Depart May 13

February 25, 2026

Hajj 2026: Sokoto Media Committee Urged to Ensure Smooth Information Flow

February 25, 2026
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
© 2026HAJJ CHRONILES

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.