Close Menu
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • Hajj News
  • Global
  • Health
  • Nahcon
  • Picture Gallery
  • Opinion
  • Videos
  • HAUSA
Facebook X (Twitter) Instagram
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram
SUBSCRIBE
  • Home
  • Hajj News

    2026/1447 Hajj Preparations Officially Launched as NAHCON Joins Global Pilgrimage Community in Closing Ceremony

    June 9, 2025

    No Lives Lost in Makkah Fire, Senate Foreign Affairs Committee Confirms

    June 9, 2025

    Pilgrimage and Leadership: How Governor Inuwa Yahaya Stood Tall Among His Peers During the 2025 Hajj – Abdulkadir Aliyu Shehu

    June 8, 2025

    From Crisis to Victory: NAHCON Chairman Called to Prostrate in Thanks for 2025 Hajj Breakthrough – By Shamwil Isah

    June 8, 2025

    Governor Abba Yusuf Disburses ₦361 Million Support to Kano Pilgrims in Mina

    June 8, 2025
  • Global

    Indonesia Plans to Acquire Land for Hajj Village Near Makkah’s Grand Mosque

    July 31, 2025

    Egypt To Halt Land Hajj Trips by 2026 Over Saudi Transport Policy Changes

    July 31, 2025

    UAE Unveils Streamlined Hajj 2026 Accreditation Process to Ensure Transparency and Quality

    July 24, 2025

    flyadeal Aims To Serve 75,000 International Hajj Pilgrims In 2025

    January 23, 2025

    Reflections on the 4th Hajj Conference and Exhibition in Jeddah – By Muhammad Ahmad Musa

    January 21, 2025
  • Health

    Gombe Muslim Pilgrim Board Commences Vaccination for 2025 Hajj Pilgrims – By Abdulqadir Aliyu Shehu

    April 28, 2025

    NAHCON Inaugurates Committee To Review National Medical Team Guidelines for Hajj 2025

    December 19, 2024

    Saudi Health Minister Strengthen Ties With Greece On Health Cooperation During Official Visit

    November 23, 2024

    Umm Al-Qura University volunteers extend help to pilgrims in Mina during Tashreeq

    June 17, 2024

    Hajj 2024: African pilgrim airlifted for emergency care

    June 14, 2024
  • Nahcon

    NAHCON Boosts Preparations for 2026 Hajj, Targets Zero Complaints in Madina

    November 27, 2025

    Investigative Journalist Exposes Coordinated Smear Campaign Against NAHCON Chairman and Leadership

    November 23, 2025

    NAHCON, Rawaf Mina Signs 2026 Hajj Agreement for Licensed Tour Operators

    November 15, 2025

    Shugaban NAHCON Ya Kaddamar da Tawagar Nusuk Masar ta Hajjin 2026

    November 15, 2025

    NAHCON Chairman Inaugurates 2026 Hajj Nusuk Masar Team

    November 14, 2025
  • Picture Gallery
  • Opinion

    When Journalism Becomes a Weapon; And Why NAHCON’s Chairman Must Be Defended

    November 24, 2025

    Fact-Check Analysis: Newspoint News Misrepresented NAHCON Chairman’s Interviews – The Real Facts Behind The Claims

    October 30, 2025

    How Professor Abdullahi Saleh Stands Tall Amid Lies, Envy, and Mercenary Journalism – By Dr Usaini Jarma

    October 17, 2025

    On Service Scrutiny, and the NAHCON Mandate in a Modern Media Dysfunction – By Ahmad Mu’azu

    October 17, 2025

    UPDATED: Integrity Under Attack: Who Is Behind the Plot Against NAHCON? By Abdulganiu Oladipo, PhD

    October 15, 2025
  • Videos
  • HAUSA
HAJJ CHRONICLES
Home » NAHCON Ta Kara Karfafa Shirye-shiryen Hajj 2026, Ta Nemi Kare Duk Wani Korafi a Madina
Hausa

NAHCON Ta Kara Karfafa Shirye-shiryen Hajj 2026, Ta Nemi Kare Duk Wani Korafi a Madina

adminBy adminNovember 27, 2025No Comments3 Mins Read
Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Email Telegram
1764255700850

Daga Shafii Sani Mohammed, Babban Jami’in Yada Labarai na NAHCON. Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON) ta kara kaimi wajen shirye-shiryen gudanar da Hajj na shekarar 2026, tare da mayar da hankali kan daidaiton aiki, hadin kai tsakanin sassa, da inganta ayyuka ga alhazai. Wannan kudiri ya kara karfi ne a wani taron tantance ayyuka da aka gudanar a Hajj House, wanda ya samu halartar Shugaban Hukumar, Kwamishinoni, Daraktoci da wakilan Acosta Media.

Karanta Wani Labarin Makamancin Wannan : Shugaban NAHCON Ya Kaddamar da Tawagar Nusuk Masar ta Hajjin 2026

A matsayin wani bangare na horon ma’aikatan NAHCON na duk wata, taken na  yau ya mayar da hankali ne kan Ayyukan Madina. Shugaban NAHCON, Farfesa Abdullahi Saleh Usman, ya bude zaman da jaddada bukatar kwarewa, gaskiya da hadin kai tsakanin dukkan sassan aiki. Ya ce Saudiyya na canza dokoki da tsarin fasaha akai-akai, lamarin da ya sanya wajibi ma’aikatan NAHCON su kasance masu sabunta ilimi da bin zamani.

“Dokoki da fasahohin Saudiyya na sauyawa kowace shekara, kuma bukatun alhazai daga Najeriya suna karuwa. Don haka dole mu kasance masu cikakken shiri, sabuwar masaniya da ingantaccen daidaiton aiki,” in ji Shugaban.

Yayin da yake tabo kalubalen shekarar da ta gabata, Farfesa Usman ya tunatar da ma’aikata cewa darussan da aka koya su zama hanya ta inganta aikin bana.

“Mun gani a inda muka samu matsaloli. Bana dole mu kara ladabi, hadin kai da jajircewa don baiwa alhazai mafi kyawun hidima,” kamar yadda yace.

Ya kuma yi bayani kan muhimmancin fahimtar gibin da aka fuskanta a bara. Shugaban ya karfafa ma’aikata kan su rika tambaya, musayar ilimi, da taimakon juna, yana mai jaddada cewa ayyukan Hajj na sauyawa kowace shekara ko da ga jami’an da ke zaune a Saudiyya.

A nasa jawabin, Kwamishinan Sashen Tsare-tsare, Bincike, Kididdiga, Bayani da dakin karatu (PRSILS), Farfesa Abubakar Yagawal, ya yi kira mai karfi da a tabbatar babu wani korafi daga alhazai a Birnin Manzon Allah, Madina.

Ya jaddada nauyin da duk wani korafi a Madina yake dauke da shi:

“Don Allah ku kokarta ku warware musu matsaloli, domin duk wani korafi a Madina, a ganina, korafi ne ga Manzon Allah ﷺ. Don haka, kada ku bari alhazanmu su samu wata matsala ko na abinci, ko masauki, ko wajen ziyara.”

Farfesa Yagawal ya bukaci jami’ai su jagoranci alhazai tun daga tashar jirgin sama ta Madina, zuwa rabon masauki da dukkan ayyukan da suka shafesu.

“Idan alhaji ya samu nutsuwa a Madina, tafiyarsa za ta kasance da annashuwa gaba daya. Amma idan ya fara da matsala a Madina, sakamakon na iya yin muni,” Inji Yagawal.

Ya yaba da jajircewar jami’an NAHCON da ke aiki tukuru a filin jirgin Madina, sannan ya bukaci karin himma:

“Na ga yadda tawagarmu ke aiki ba dare ba rana a Madina. Amma don Allah, ku ninka kokarinku wajen faranta ran alhazai.”

Tun da farko a cikin taron, Daraktan Ma’aikata da Albarkatun Dan Adam, Alhaji Alidu Shutti, ya yi maraba da mahalarta taron kuma ya tabbatar da kudirin Hukumar na karfafa gwiwar ma’aikata kafin Hajj 2026.

Ya shawarci ma’aikata da su shiga sosai cikin taron, yana mai bayyana cewa wasu daga cikin gabatarwar da ake yi a irin wadannan taruka za su zama tambayoyi a jarabawar karin girma da Hukumar za ta gudanar.

Zaman ya sake tabbatar da kudirin NAHCON na inganta ayyuka, daidaiton aiki da samar da kyakkyawar tafiyar Hajj ga alhazai daga Najeriya. Tare da Shugabanci na jaddada tsari, hadin kai da ingantacciyar hidima musamman a Madina, inda yawanci tafiyar Hajj ke farawa NAHCON na fatan zarce dukkan matakai da na shekarun baya yayin da ake shirin gudanar da Hajj 2026 mai nasara.

Ma'aikata Madina NAHCON
Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp

Related Posts

NAHCON Boosts Preparations for 2026 Hajj, Targets Zero Complaints in Madina

November 27, 2025

Bincike Ya Nuna Yadda Ake Kirkirar Labaran Karya Don A Bata Sunan Shugaban NAHCON

November 25, 2025

AHMSP Clarifies Issues Raised in Independent Hajj Reporters’ Publication

November 15, 2025
Leave A Reply Cancel Reply

Don't Miss
Nahcon

NAHCON Boosts Preparations for 2026 Hajj, Targets Zero Complaints in Madina

By adminNovember 27, 20250

By Shafii Sani Mohammed The National Hajj Commission of Nigeria (NAHCON) has intensified its preparations…

NAHCON Ta Kara Karfafa Shirye-shiryen Hajj 2026, Ta Nemi Kare Duk Wani Korafi a Madina

November 27, 2025

Bincike Ya Nuna Yadda Ake Kirkirar Labaran Karya Don A Bata Sunan Shugaban NAHCON

November 25, 2025

Kwara Announces Final Deadline for 2026 Hajj Payment

November 25, 2025
Stay In Touch
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • WhatsApp
Our Picks

NAHCON Boosts Preparations for 2026 Hajj, Targets Zero Complaints in Madina

November 27, 2025

NAHCON Ta Kara Karfafa Shirye-shiryen Hajj 2026, Ta Nemi Kare Duk Wani Korafi a Madina

November 27, 2025

Bincike Ya Nuna Yadda Ake Kirkirar Labaran Karya Don A Bata Sunan Shugaban NAHCON

November 25, 2025

Kwara Announces Final Deadline for 2026 Hajj Payment

November 25, 2025
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
© 2025HAJJ CHRONILES

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.