Close Menu
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • Hajj News
  • Global
  • Health
  • Nahcon
  • Picture Gallery
  • Opinion
  • Videos
  • HAUSA
Facebook X (Twitter) Instagram
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram
SUBSCRIBE
  • Home
  • Hajj News

    2026/1447 Hajj Preparations Officially Launched as NAHCON Joins Global Pilgrimage Community in Closing Ceremony

    June 9, 2025

    No Lives Lost in Makkah Fire, Senate Foreign Affairs Committee Confirms

    June 9, 2025

    Pilgrimage and Leadership: How Governor Inuwa Yahaya Stood Tall Among His Peers During the 2025 Hajj – Abdulkadir Aliyu Shehu

    June 8, 2025

    From Crisis to Victory: NAHCON Chairman Called to Prostrate in Thanks for 2025 Hajj Breakthrough – By Shamwil Isah

    June 8, 2025

    Governor Abba Yusuf Disburses ₦361 Million Support to Kano Pilgrims in Mina

    June 8, 2025
  • Global

    Indonesia Plans to Acquire Land for Hajj Village Near Makkah’s Grand Mosque

    July 31, 2025

    Egypt To Halt Land Hajj Trips by 2026 Over Saudi Transport Policy Changes

    July 31, 2025

    UAE Unveils Streamlined Hajj 2026 Accreditation Process to Ensure Transparency and Quality

    July 24, 2025

    flyadeal Aims To Serve 75,000 International Hajj Pilgrims In 2025

    January 23, 2025

    Reflections on the 4th Hajj Conference and Exhibition in Jeddah – By Muhammad Ahmad Musa

    January 21, 2025
  • Health

    Gombe Muslim Pilgrim Board Commences Vaccination for 2025 Hajj Pilgrims – By Abdulqadir Aliyu Shehu

    April 28, 2025

    NAHCON Inaugurates Committee To Review National Medical Team Guidelines for Hajj 2025

    December 19, 2024

    Saudi Health Minister Strengthen Ties With Greece On Health Cooperation During Official Visit

    November 23, 2024

    Umm Al-Qura University volunteers extend help to pilgrims in Mina during Tashreeq

    June 17, 2024

    Hajj 2024: African pilgrim airlifted for emergency care

    June 14, 2024
  • Nahcon

    NAHCON Approves Two 23kg Checked Bags for 2026 Hajj Pilgrims

    January 1, 2026

    NAHCON Begins Preparations for 2026 Hajj Medical Operations

    December 30, 2025

    No Contract Rollover: NAHCON Sets Record Straight on 2026 Hajj Procurement

    December 18, 2025

    The Penumbra of Influence: How Mercenary Journalism Built False Narratives Around NAHCON By Ahmad Mu’azu

    December 16, 2025

    NAHCON Opens Application Portal for 2026 National Medical Team

    December 12, 2025
  • Picture Gallery
  • Opinion

    The Need to Reintroduce Capacity-Building Workshops for Hajj Information Managers in Nigeria By Faruku Umar

    January 13, 2026

    Integrity, Discipline and Tireless Communication: Kano Pilgrims Board Shines Under Dedicated Leadership

    January 13, 2026

    NAHCON At 20: The Imperative of Repositioning Nigeria’s Hajj and Umrah Sector – Ibrahim Ishaq Jae

    January 12, 2026

    2026 Hajj Crisis: NAHCON, GACA Set to Clash Over Pilgrims’ Airlift

    January 11, 2026

    Man of the year: Professor Abdullahi Saleh, the game Changer – By Sagir Huguma

    January 3, 2026
  • Videos
  • HAUSA
HAJJ CHRONICLES
Home » NAHCON Ta Kara Karfafa Shirye-shiryen Hajj 2026, Ta Nemi Kare Duk Wani Korafi a Madina
Hausa

NAHCON Ta Kara Karfafa Shirye-shiryen Hajj 2026, Ta Nemi Kare Duk Wani Korafi a Madina

adminBy adminNovember 27, 2025No Comments3 Mins Read
Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Email Telegram
1764255700850

Daga Shafii Sani Mohammed, Babban Jami’in Yada Labarai na NAHCON. Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON) ta kara kaimi wajen shirye-shiryen gudanar da Hajj na shekarar 2026, tare da mayar da hankali kan daidaiton aiki, hadin kai tsakanin sassa, da inganta ayyuka ga alhazai. Wannan kudiri ya kara karfi ne a wani taron tantance ayyuka da aka gudanar a Hajj House, wanda ya samu halartar Shugaban Hukumar, Kwamishinoni, Daraktoci da wakilan Acosta Media.

Karanta Wani Labarin Makamancin Wannan : Shugaban NAHCON Ya Kaddamar da Tawagar Nusuk Masar ta Hajjin 2026

A matsayin wani bangare na horon ma’aikatan NAHCON na duk wata, taken na  yau ya mayar da hankali ne kan Ayyukan Madina. Shugaban NAHCON, Farfesa Abdullahi Saleh Usman, ya bude zaman da jaddada bukatar kwarewa, gaskiya da hadin kai tsakanin dukkan sassan aiki. Ya ce Saudiyya na canza dokoki da tsarin fasaha akai-akai, lamarin da ya sanya wajibi ma’aikatan NAHCON su kasance masu sabunta ilimi da bin zamani.

“Dokoki da fasahohin Saudiyya na sauyawa kowace shekara, kuma bukatun alhazai daga Najeriya suna karuwa. Don haka dole mu kasance masu cikakken shiri, sabuwar masaniya da ingantaccen daidaiton aiki,” in ji Shugaban.

Yayin da yake tabo kalubalen shekarar da ta gabata, Farfesa Usman ya tunatar da ma’aikata cewa darussan da aka koya su zama hanya ta inganta aikin bana.

“Mun gani a inda muka samu matsaloli. Bana dole mu kara ladabi, hadin kai da jajircewa don baiwa alhazai mafi kyawun hidima,” kamar yadda yace.

Ya kuma yi bayani kan muhimmancin fahimtar gibin da aka fuskanta a bara. Shugaban ya karfafa ma’aikata kan su rika tambaya, musayar ilimi, da taimakon juna, yana mai jaddada cewa ayyukan Hajj na sauyawa kowace shekara ko da ga jami’an da ke zaune a Saudiyya.

A nasa jawabin, Kwamishinan Sashen Tsare-tsare, Bincike, Kididdiga, Bayani da dakin karatu (PRSILS), Farfesa Abubakar Yagawal, ya yi kira mai karfi da a tabbatar babu wani korafi daga alhazai a Birnin Manzon Allah, Madina.

Ya jaddada nauyin da duk wani korafi a Madina yake dauke da shi:

“Don Allah ku kokarta ku warware musu matsaloli, domin duk wani korafi a Madina, a ganina, korafi ne ga Manzon Allah ﷺ. Don haka, kada ku bari alhazanmu su samu wata matsala ko na abinci, ko masauki, ko wajen ziyara.”

Farfesa Yagawal ya bukaci jami’ai su jagoranci alhazai tun daga tashar jirgin sama ta Madina, zuwa rabon masauki da dukkan ayyukan da suka shafesu.

“Idan alhaji ya samu nutsuwa a Madina, tafiyarsa za ta kasance da annashuwa gaba daya. Amma idan ya fara da matsala a Madina, sakamakon na iya yin muni,” Inji Yagawal.

Ya yaba da jajircewar jami’an NAHCON da ke aiki tukuru a filin jirgin Madina, sannan ya bukaci karin himma:

“Na ga yadda tawagarmu ke aiki ba dare ba rana a Madina. Amma don Allah, ku ninka kokarinku wajen faranta ran alhazai.”

Tun da farko a cikin taron, Daraktan Ma’aikata da Albarkatun Dan Adam, Alhaji Alidu Shutti, ya yi maraba da mahalarta taron kuma ya tabbatar da kudirin Hukumar na karfafa gwiwar ma’aikata kafin Hajj 2026.

Ya shawarci ma’aikata da su shiga sosai cikin taron, yana mai bayyana cewa wasu daga cikin gabatarwar da ake yi a irin wadannan taruka za su zama tambayoyi a jarabawar karin girma da Hukumar za ta gudanar.

Zaman ya sake tabbatar da kudirin NAHCON na inganta ayyuka, daidaiton aiki da samar da kyakkyawar tafiyar Hajj ga alhazai daga Najeriya. Tare da Shugabanci na jaddada tsari, hadin kai da ingantacciyar hidima musamman a Madina, inda yawanci tafiyar Hajj ke farawa NAHCON na fatan zarce dukkan matakai da na shekarun baya yayin da ake shirin gudanar da Hajj 2026 mai nasara.

Ma'aikata Madina NAHCON
Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp

Related Posts

Nagarta, Da’a da Sadarwa Cikin Jajircewa: Hukumar Alhazan Kano na Haskakawa ƙarƙashin Jagoranci Nagari

January 13, 2026

Rikicin Jigilar Alhazan 2026: Zargin Makircin Cikin Gida A NAHCON Na Barazana Ga Yarjejeniyar Sufurin Jirage Tsakanin Najeriya Da Saudia

January 12, 2026

Hajjin 2026: Jihar Gombe Ta Fara Gwajin Lafiya na Tilas ga Maniyyatan – Daga Abdulkadir Aliyu Shehu

January 12, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

Don't Miss
SPWA

Hajj 2026: Lagos begins medical screening for intending pilgrims, appoints LGA coordinators

By adminJanuary 14, 20260

The Lagos State Government has commenced medical screening for all intending pilgrims performing the 2026…

Hajj 2026: Kano Pilgrims Board Announces Deadline for Data Capturing

January 14, 2026

The Need to Reintroduce Capacity-Building Workshops for Hajj Information Managers in Nigeria By Faruku Umar

January 13, 2026

Nagarta, Da’a da Sadarwa Cikin Jajircewa: Hukumar Alhazan Kano na Haskakawa ƙarƙashin Jagoranci Nagari

January 13, 2026
Stay In Touch
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • WhatsApp
Our Picks

Hajj 2026: Lagos begins medical screening for intending pilgrims, appoints LGA coordinators

January 14, 2026

Hajj 2026: Kano Pilgrims Board Announces Deadline for Data Capturing

January 14, 2026

The Need to Reintroduce Capacity-Building Workshops for Hajj Information Managers in Nigeria By Faruku Umar

January 13, 2026

Nagarta, Da’a da Sadarwa Cikin Jajircewa: Hukumar Alhazan Kano na Haskakawa ƙarƙashin Jagoranci Nagari

January 13, 2026
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
© 2026HAJJ CHRONILES

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.