Close Menu
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • Hajj News
  • Global
  • Health
  • Nahcon
  • Picture Gallery
  • Opinion
  • Videos
  • HAUSA
Facebook X (Twitter) Instagram
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram
SUBSCRIBE
  • Home
  • Hajj News

    2026/1447 Hajj Preparations Officially Launched as NAHCON Joins Global Pilgrimage Community in Closing Ceremony

    June 9, 2025

    No Lives Lost in Makkah Fire, Senate Foreign Affairs Committee Confirms

    June 9, 2025

    Pilgrimage and Leadership: How Governor Inuwa Yahaya Stood Tall Among His Peers During the 2025 Hajj – Abdulkadir Aliyu Shehu

    June 8, 2025

    From Crisis to Victory: NAHCON Chairman Called to Prostrate in Thanks for 2025 Hajj Breakthrough – By Shamwil Isah

    June 8, 2025

    Governor Abba Yusuf Disburses ₦361 Million Support to Kano Pilgrims in Mina

    June 8, 2025
  • Global

    Indonesia Plans to Acquire Land for Hajj Village Near Makkah’s Grand Mosque

    July 31, 2025

    Egypt To Halt Land Hajj Trips by 2026 Over Saudi Transport Policy Changes

    July 31, 2025

    UAE Unveils Streamlined Hajj 2026 Accreditation Process to Ensure Transparency and Quality

    July 24, 2025

    flyadeal Aims To Serve 75,000 International Hajj Pilgrims In 2025

    January 23, 2025

    Reflections on the 4th Hajj Conference and Exhibition in Jeddah – By Muhammad Ahmad Musa

    January 21, 2025
  • Health

    Gombe Muslim Pilgrim Board Commences Vaccination for 2025 Hajj Pilgrims – By Abdulqadir Aliyu Shehu

    April 28, 2025

    NAHCON Inaugurates Committee To Review National Medical Team Guidelines for Hajj 2025

    December 19, 2024

    Saudi Health Minister Strengthen Ties With Greece On Health Cooperation During Official Visit

    November 23, 2024

    Umm Al-Qura University volunteers extend help to pilgrims in Mina during Tashreeq

    June 17, 2024

    Hajj 2024: African pilgrim airlifted for emergency care

    June 14, 2024
  • Nahcon

    NAHCON Approves Two 23kg Checked Bags for 2026 Hajj Pilgrims

    January 1, 2026

    NAHCON Begins Preparations for 2026 Hajj Medical Operations

    December 30, 2025

    No Contract Rollover: NAHCON Sets Record Straight on 2026 Hajj Procurement

    December 18, 2025

    The Penumbra of Influence: How Mercenary Journalism Built False Narratives Around NAHCON By Ahmad Mu’azu

    December 16, 2025

    NAHCON Opens Application Portal for 2026 National Medical Team

    December 12, 2025
  • Picture Gallery
  • Opinion

    The Need to Reintroduce Capacity-Building Workshops for Hajj Information Managers in Nigeria By Faruku Umar

    January 13, 2026

    Integrity, Discipline and Tireless Communication: Kano Pilgrims Board Shines Under Dedicated Leadership

    January 13, 2026

    NAHCON At 20: The Imperative of Repositioning Nigeria’s Hajj and Umrah Sector – Ibrahim Ishaq Jae

    January 12, 2026

    2026 Hajj Crisis: NAHCON, GACA Set to Clash Over Pilgrims’ Airlift

    January 11, 2026

    Man of the year: Professor Abdullahi Saleh, the game Changer – By Sagir Huguma

    January 3, 2026
  • Videos
  • HAUSA
HAJJ CHRONICLES
Home » Hajj Chronicles Ta Fallasa Zargin Makircin Cikin Gida da Ake Yi Don Kawo Matsala Ga Shugabancin NAHCON
Hausa

Hajj Chronicles Ta Fallasa Zargin Makircin Cikin Gida da Ake Yi Don Kawo Matsala Ga Shugabancin NAHCON

adminBy adminDecember 3, 2025No Comments3 Mins Read
Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Email Telegram
1764787661970

Wani bincike na musamman da Jaridar  Hajj Chronicles ta gudanar ya gano abin da ake zargin wani shiri ne na cikin gida da nufin lalata ayyukan Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON), bisa ga wasu muhimman takardu da aka fallasa da kuma tattaunawa da wasu manyan jami’an gwamnati da suka san al’amuran da ke faruwa a halin yanzu.

KARANTA LABARI MAKAMANCIN WANNAN : Bincike Ya Nuna Yadda Ake Kirkirar Labaran Karya Don A Bata Sunan Shugaban NAHCON

Wadannan takardu da ake kyautata zaton sun fito ne daga wani rahoton binciken leken asiri na cikin gida sun nuna cewa akwai wata hanyar sadarwa ta wasu mutane a cikin Hukumar da kewaye da ita da ake zargin suna kokarin haifar da rudani a harkokin gudanarwa kafin fara shirin Hajjin 2026.

Takardun na nuni da cewa wannan zargin makircin yana da nufin raunana amincewar jama’a ga shugabancin NAHCON da kuma jefa Fadar Shugaban Kasa cikin mawuyacin hali musamman tsakanin al’ummar Musulmi a Najeriya.

A tsakiyar wannan binciken akwai Shugaban NAHCON, wanda majiyoyi suka bayyana a matsayin mutum mai rikon gaskiya, tsantseni, da shugabanci mai bin umarnin Shugaban Kasa cikin gaskiya da tsari.

A cewar rahoton da aka fallasa, kin amincewarsa da tasirin wasu mutane wajen sarrafa harkokin kudi da tafiyar da hukumar ya haifar da matsin lamba daga wadanda ke neman iko da muhimman bangarorin hukumar.

Wani babban jami’i da ya bukaci a sakaya sunansa saboda tsananin mahimmancin lamarin ya bayyana cewa:

“Kin amincewar Shugaban Hukumar da sabawa ka’idoji ya janyo kokarin kirkirar matsalolin dagula aikinsa.”

Babban abin da rahoton ya bankado shi ne sauyin tsarin da aka yi kwanan nan, inda kulawar NAHCON ta koma daga Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF) zuwa Ofishin Mataimakin Shugaban Kasa. Tun bayan wannan sauyi, masu ruwa da tsaki sun ruwaito karuwar karya ka’idojin aiki, ciki har da yadda wasu kananan jami’ai ke wucewa shugaban kai tsaye suna mikawa manyan ofisoshi bayanan sirri ba tare da izini ba.

Masana sun gargadi cewa irin wadannan dabi’u, idan ba a magance su da gaggawa ba, na iya rusa tsarin jagoranci a cikin Hukumar, su takaita yanke shawara, su kuma kawo tsaiko wajen shirin gudanar da Hajjin bana.

Masu fahimtar bayanan leken asiri sun yi gargadin cewa duk wani yunkuri na tayar da hankalin NAHCON zai iya haifar da mummunan tasiri ga kasa baki daya.

Yayin da aikin Hajin 2026 ke dada karatowa, duk wata matsala ko tsaiko a shiri na iya janyo fushin jama’a musamman saboda mahimmancin addini da siyasa da ke tattare da Hajj a Najeriya.

A tarihi, duk wata gazawa a manyan cibiyoyin hidimar jama’a kan janyo wa Shugaban Kasa suka da zargi.

Masana sun yi nuni da cewa matsala a tafiyar da al’amuran Hajj na iya rikidewa zuwa matsalar siyasa da zamantakewa.

Rahoton da aka fallasa ya ba da shawarar a yi nazari cikin gaggawa kan tsarin kulawar NAHCON.

Shawarwarin da aka bayar sun haɗa da mayar da hukumar ƙarƙashin ofishin Sakataren gwamnatin tarayya, ko kuma a mika Hukumar Kiristoci zuwa Ofishin Mataimakin Shugaban Kasa domin daidaito.

Manyan jami’an da Hajj Chronicles ta tattauna da su sun jaddada cewa gaggawar daukar mataki na da muhimmanci don kaucewa lalata suna, tabarbarewar tsarin aiki, ko tsaikon da zai iya shafar shirin Hajjin shekara mai zuwa.

Hajj Chronicles za ta ci gaba da bibiyar lamarin tare da neman karin bayani daga hukumomin da abin ya shafa.

A lokacin wallafa wannan rahoto, NAHCON, Ofishin Sakataren Gwamnatin tarayya, da Ofishin Mataimakin Shugaban Kasa ba su amsa bukatar karin bayani ba.

 

Bincike Hajin 2026 Makirci NAHCON
Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp

Related Posts

Nagarta, Da’a da Sadarwa Cikin Jajircewa: Hukumar Alhazan Kano na Haskakawa ƙarƙashin Jagoranci Nagari

January 13, 2026

Rikicin Jigilar Alhazan 2026: Zargin Makircin Cikin Gida A NAHCON Na Barazana Ga Yarjejeniyar Sufurin Jirage Tsakanin Najeriya Da Saudia

January 12, 2026

Hajjin 2026: Jihar Gombe Ta Fara Gwajin Lafiya na Tilas ga Maniyyatan – Daga Abdulkadir Aliyu Shehu

January 12, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

Don't Miss
SPWA

Hajj 2026: Lagos begins medical screening for intending pilgrims, appoints LGA coordinators

By adminJanuary 14, 20260

The Lagos State Government has commenced medical screening for all intending pilgrims performing the 2026…

Hajj 2026: Kano Pilgrims Board Announces Deadline for Data Capturing

January 14, 2026

The Need to Reintroduce Capacity-Building Workshops for Hajj Information Managers in Nigeria By Faruku Umar

January 13, 2026

Nagarta, Da’a da Sadarwa Cikin Jajircewa: Hukumar Alhazan Kano na Haskakawa ƙarƙashin Jagoranci Nagari

January 13, 2026
Stay In Touch
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • WhatsApp
Our Picks

Hajj 2026: Lagos begins medical screening for intending pilgrims, appoints LGA coordinators

January 14, 2026

Hajj 2026: Kano Pilgrims Board Announces Deadline for Data Capturing

January 14, 2026

The Need to Reintroduce Capacity-Building Workshops for Hajj Information Managers in Nigeria By Faruku Umar

January 13, 2026

Nagarta, Da’a da Sadarwa Cikin Jajircewa: Hukumar Alhazan Kano na Haskakawa ƙarƙashin Jagoranci Nagari

January 13, 2026
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
© 2026HAJJ CHRONILES

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.