Close Menu
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • Hajj News
  • Global
  • Health
  • Nahcon
  • Picture Gallery
  • Opinion
  • Videos
  • HAUSA
Facebook X (Twitter) Instagram
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram
SUBSCRIBE
  • Home
  • Hajj News

    2026/1447 Hajj Preparations Officially Launched as NAHCON Joins Global Pilgrimage Community in Closing Ceremony

    June 9, 2025

    No Lives Lost in Makkah Fire, Senate Foreign Affairs Committee Confirms

    June 9, 2025

    Pilgrimage and Leadership: How Governor Inuwa Yahaya Stood Tall Among His Peers During the 2025 Hajj – Abdulkadir Aliyu Shehu

    June 8, 2025

    From Crisis to Victory: NAHCON Chairman Called to Prostrate in Thanks for 2025 Hajj Breakthrough – By Shamwil Isah

    June 8, 2025

    Governor Abba Yusuf Disburses ₦361 Million Support to Kano Pilgrims in Mina

    June 8, 2025
  • Global

    Indonesia Plans to Acquire Land for Hajj Village Near Makkah’s Grand Mosque

    July 31, 2025

    Egypt To Halt Land Hajj Trips by 2026 Over Saudi Transport Policy Changes

    July 31, 2025

    UAE Unveils Streamlined Hajj 2026 Accreditation Process to Ensure Transparency and Quality

    July 24, 2025

    flyadeal Aims To Serve 75,000 International Hajj Pilgrims In 2025

    January 23, 2025

    Reflections on the 4th Hajj Conference and Exhibition in Jeddah – By Muhammad Ahmad Musa

    January 21, 2025
  • Health

    Gombe Muslim Pilgrim Board Commences Vaccination for 2025 Hajj Pilgrims – By Abdulqadir Aliyu Shehu

    April 28, 2025

    NAHCON Inaugurates Committee To Review National Medical Team Guidelines for Hajj 2025

    December 19, 2024

    Saudi Health Minister Strengthen Ties With Greece On Health Cooperation During Official Visit

    November 23, 2024

    Umm Al-Qura University volunteers extend help to pilgrims in Mina during Tashreeq

    June 17, 2024

    Hajj 2024: African pilgrim airlifted for emergency care

    June 14, 2024
  • Nahcon

    NAHCON Chairman Strengthens Ties with Saudi Embassy Ahead of 2026 Hajj

    February 27, 2026

    NAHCON Signs 2026 Hajj Airlift Agreement, Emphasizes Compliance and Efficiency

    February 25, 2026

    No Additional Slots for 2026 Hajj, Says NAHCON as Visa Issuance Nears

    February 24, 2026

    NAHCON Unveils Reforms, Clarifies Quota Adjustment Ahead of 2026 Hajj – By Abdulbasit Abba

    February 23, 2026

    NAHCON Raises Alarm Over Fake Facebook Account Impersonating Chairman

    February 22, 2026
  • Picture Gallery
  • Opinion

    Nigeria Hajj Industry: Back To Square One – By Abubakar Jidda Usman

    February 11, 2026

    NAHCON Reconciliation Viewed as Positive Step for Hajj Administration – By Muhammad Sulaiman Gama

    February 2, 2026

    NAHCON Board’s Vote of No Confidence: A Mask for Self-Interest.

    February 1, 2026

    Nigeria Hajj Industry: When Would Pilgrims’ Interest Supercede Personal Interest of Handlers and Stakeholders

    January 31, 2026

    Who Is Afraid of Pakistan? By Faruku Umar

    January 31, 2026
  • Videos
  • HAUSA
HAJJ CHRONICLES
Home » Hajjin 2026: Jihar Gombe Ta Fara Gwajin Lafiya na Tilas ga Maniyyatan – Daga Abdulkadir Aliyu Shehu
Hausa

Hajjin 2026: Jihar Gombe Ta Fara Gwajin Lafiya na Tilas ga Maniyyatan – Daga Abdulkadir Aliyu Shehu

adminBy adminJanuary 12, 2026No Comments4 Mins Read
Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Email Telegram
IMG 20260112 WA0015

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Gombe ta kaddamar da aikin gwajin lafiya ga maniyyatan Hajjin 2026, a matsayin wani muhimmin mataki na tabbatar da cewa dukkan maniyyatan jihar suna cikin koshin lafiya domin gudanar da ibadun Hajji masu bukatar ƙarfi da juriya a Ƙasar Saudiyya.

Da yake jawabi a wajen bikin kaddamar da shirin, Babban Sakataren Hukumar, Alhaji Sa’adu Hassan, ya bayyana cewa gwajin lafiyar wajibi ne bisa umarnin hukumomin Saudiyya, inda ya jaddada cewa dole ne duk maniyyata su bi ka’idojin ba tare da wani rangwame ba.

A cewarsa, wannan tsari na daga cikin matakan lafiya da tsaro na ƙasa da ƙasa da aka kafa domin kare rayukan alhazai da kuma tabbatar da gudanar da aikin Hajji cikin sauƙi.

Ya kara da cewa ibadun Hajji na bukatar ƙarfi da juriya sosai, don haka lafiyar jiki na da matuƙar muhimmanci.

Alhaji Sa’adu Hassan ya bayyana cewa duk maniyyacin da aka gano yana da babbar matsalar lafiya ba za a bari ya je Hajjin 2026 ba. Ya ce ko da yake wannan mataki yana da wahala, amma wajibi ne domin kauce wa matsalolin gaggawa na lafiya da kuma kare jin daɗin maniyyata.

Ya kuma bayyana cewa ba za a yarda mata masu juna biyu su je Hajjin 2026 ba, sakamakon barazanar lafiya ga uwa da jaririn cikinta, la’akari da tsananin wahalhalun ibadun Hajji da kuma yanayin zafin ƙasar Saudiyya.

Sakataren Zartarwar ya ce za a gudanar da gwajin lafiyar ne kashi-kashi domin tabbatar da cikakken tsari da gaskiya. Ya bayyana cewa an fara zagaye na farko a halin yanzu, yayin da za a gudanar da zagaye na biyu bayan watan Ramadan.

Ya ce zagaye na biyu yana da matuƙar muhimmanci domin tabbatar da cewa babu wata mai juna biyu da za ta tafi aikin Hajji, hakan zai hana matsalolin lafiya na gaggawa a minti na ƙarshe tare da tabbatar da bin dokokin Hajjin Saudiyya gaba ɗaya.

Sa’adu Hassan ya yi kira ga duk maniyyata da su ba da cikakken haɗin kai ga jami’an lafiya tare da bayar da sahihin bayani kan lafiyarsu, yana mai gargaɗin cewa ɓoye matsalar lafiya na iya kaiwa ga hana mutum zuwa aikin Hajji.

Ya sake jaddada kudurin Gwamnatin Jihar Gombe da Hukumar Jin Daɗin Alhazai na tabbatar da tsaro, walwala da jin daɗin maniyyata, yana mai tabbatar da cewa Hukumar za ta gudanar da Hajjin 2026 cikin nasara ba tare da wata tangarda ba.

A nasa jawabin, Babban Daraktan Asibitin Kwararru na Gombe, Dakta Sambo Dawa, ya tabbatarwa maniyyata cewa an tanadi dukkan abubuwan da suka dace domin gudanar da gwajin lafiyar cikin sauƙi da inganci.

Dakta Dawa ya ce an tura kwararrun jami’an lafiya da suka hada da likitoci, ma’aikatan jinya da sauran ma’aikatan lafiya domin gudanar da gwajin, domin tabbatar da cewa an duba kowane maniyyaci yadda ya kamata.

Ya kara da cewa an samar da kayayyakin aikin lafiya na zamani da dakunan gwaji domin taimakawa wajen yin sahihin bincike da tantance lafiyar maniyyata, yana mai jaddada kudurin asibitin na kiyaye mafi girman matakan aikin lafiya a duk tsawon shirin.

Babban Daraktan ya tabbatar wa maniyyata cewa za a gudanar da gwajin cikin adalci, sirri da girmama mutuncin dan Adam, yana mai cewa manufar shirin ba hana kowa yin Hajji ba ce, sai dai tabbatar da tsaro da shiri na gari.

Ya bukaci maniyyata da su dauki gwajin lafiyar a matsayin matakin kariya da rigakafi, yana mai cewa gano matsalar lafiya da wuri na iya ba da damar samun magani cikin lokaci tare da kara yiwuwar halartar Hajji a nan gaba.

Dakta Dawa ya kuma jaddada muhimmancin kula da lafiya tun kafin tafiya, yana mai kira ga maniyyata da su bi dukkan shawarwari da umarnin likitoci da za a ba su yayin gwajin.

Wasu daga cikin maniyyatan da suka halarci gwajin sun yabawa Hukumar da Gwamnatin Jihar Gombe bisa fifita lafiyarsu da tsaronsu, suna masu bayyana shirin a matsayin wanda ya zo a kan lokaci kuma ya zama dole.

Wasu kuma sun yi kira da a rika ci gaba da wayar da kan maniyyata kan kula da lafiya, musamman wajen sarrafa cututtuka masu tsanani da kuma kiyaye lafiyar jiki kafin tafiya Hajji.

Gaba ɗaya, fara aikin gwajin lafiyar maniyyata ya zama wani muhimmin mataki a shirye-shiryen Hajjin 2026. Tare da tsauraran matakan lafiya, goyon bayan kwararrun jami’an lafiya da kuma jajircewar hukumomi, Jihar Gombe na fatan tabbatar da Hajji mai tsaro, nasara da cikar ruhi ga dukkan maniyyatan da suka cancanta.

Gombe Gwajin Lafiya Hajj 2026 Maniyyata
Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp

Related Posts

NAHCON Chairman Strengthens Ties with Saudi Embassy Ahead of 2026 Hajj

February 27, 2026

Jigawa Pilgrims Board Seeks Smooth Immigration Process for 2026 Hajj

February 26, 2026

2026 Hajj: First Batch of Kano Pilgrims to Depart May 13

February 25, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

Don't Miss
Nahcon

NAHCON Chairman Strengthens Ties with Saudi Embassy Ahead of 2026 Hajj

By adminFebruary 27, 20260

By Suwaiba Ahmad The Chairman/CEO of the National Hajj Commission of Nigeria (NAHCON), Ambassador Ismail…

Jigawa Pilgrims Board Seeks Smooth Immigration Process for 2026 Hajj

February 26, 2026

2026 Hajj: First Batch of Kano Pilgrims to Depart May 13

February 25, 2026

Hajj 2026: Sokoto Media Committee Urged to Ensure Smooth Information Flow

February 25, 2026
Stay In Touch
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • WhatsApp
Our Picks

NAHCON Chairman Strengthens Ties with Saudi Embassy Ahead of 2026 Hajj

February 27, 2026

Jigawa Pilgrims Board Seeks Smooth Immigration Process for 2026 Hajj

February 26, 2026

2026 Hajj: First Batch of Kano Pilgrims to Depart May 13

February 25, 2026

Hajj 2026: Sokoto Media Committee Urged to Ensure Smooth Information Flow

February 25, 2026
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
© 2026HAJJ CHRONILES

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.