Close Menu
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • Hajj News
  • Global
  • Health
  • Nahcon
  • Picture Gallery
  • Opinion
  • Videos
  • HAUSA
Facebook X (Twitter) Instagram
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram
SUBSCRIBE
  • Home
  • Hajj News

    2026/1447 Hajj Preparations Officially Launched as NAHCON Joins Global Pilgrimage Community in Closing Ceremony

    June 9, 2025

    No Lives Lost in Makkah Fire, Senate Foreign Affairs Committee Confirms

    June 9, 2025

    Pilgrimage and Leadership: How Governor Inuwa Yahaya Stood Tall Among His Peers During the 2025 Hajj – Abdulkadir Aliyu Shehu

    June 8, 2025

    From Crisis to Victory: NAHCON Chairman Called to Prostrate in Thanks for 2025 Hajj Breakthrough – By Shamwil Isah

    June 8, 2025

    Governor Abba Yusuf Disburses ₦361 Million Support to Kano Pilgrims in Mina

    June 8, 2025
  • Global

    Indonesia Plans to Acquire Land for Hajj Village Near Makkah’s Grand Mosque

    July 31, 2025

    Egypt To Halt Land Hajj Trips by 2026 Over Saudi Transport Policy Changes

    July 31, 2025

    UAE Unveils Streamlined Hajj 2026 Accreditation Process to Ensure Transparency and Quality

    July 24, 2025

    flyadeal Aims To Serve 75,000 International Hajj Pilgrims In 2025

    January 23, 2025

    Reflections on the 4th Hajj Conference and Exhibition in Jeddah – By Muhammad Ahmad Musa

    January 21, 2025
  • Health

    Gombe Muslim Pilgrim Board Commences Vaccination for 2025 Hajj Pilgrims – By Abdulqadir Aliyu Shehu

    April 28, 2025

    NAHCON Inaugurates Committee To Review National Medical Team Guidelines for Hajj 2025

    December 19, 2024

    Saudi Health Minister Strengthen Ties With Greece On Health Cooperation During Official Visit

    November 23, 2024

    Umm Al-Qura University volunteers extend help to pilgrims in Mina during Tashreeq

    June 17, 2024

    Hajj 2024: African pilgrim airlifted for emergency care

    June 14, 2024
  • Nahcon

    NAHCON Chairman Strengthens Ties with Saudi Embassy Ahead of 2026 Hajj

    February 27, 2026

    NAHCON Signs 2026 Hajj Airlift Agreement, Emphasizes Compliance and Efficiency

    February 25, 2026

    No Additional Slots for 2026 Hajj, Says NAHCON as Visa Issuance Nears

    February 24, 2026

    NAHCON Unveils Reforms, Clarifies Quota Adjustment Ahead of 2026 Hajj – By Abdulbasit Abba

    February 23, 2026

    NAHCON Raises Alarm Over Fake Facebook Account Impersonating Chairman

    February 22, 2026
  • Picture Gallery
  • Opinion

    Nigeria Hajj Industry: Back To Square One – By Abubakar Jidda Usman

    February 11, 2026

    NAHCON Reconciliation Viewed as Positive Step for Hajj Administration – By Muhammad Sulaiman Gama

    February 2, 2026

    NAHCON Board’s Vote of No Confidence: A Mask for Self-Interest.

    February 1, 2026

    Nigeria Hajj Industry: When Would Pilgrims’ Interest Supercede Personal Interest of Handlers and Stakeholders

    January 31, 2026

    Who Is Afraid of Pakistan? By Faruku Umar

    January 31, 2026
  • Videos
  • HAUSA
HAJJ CHRONICLES
Home » NAHCON, Ma’aikatar Hajji ta Saudiyya Sun Gudanar da Muhimmiyar Tattaunawa kan Shirye-shiryen Hajjin 2026
Hausa

NAHCON, Ma’aikatar Hajji ta Saudiyya Sun Gudanar da Muhimmiyar Tattaunawa kan Shirye-shiryen Hajjin 2026

adminBy adminJanuary 21, 2026No Comments3 Mins Read
Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Email Telegram
1769016500875

Daga Shafii Sani Mohammed Da Abdul Abba Hukumar Alhazai ta Ƙasa ta Najeriya (NAHCON) ta karɓi wata babbar tawaga daga Masarautar Saudiyya, Ma’aikatar Hajji da Umrah, ƙarƙashin jagorancin Farfesa Dakta Ghassan Al-Nuaimi, a Hajj House da ke Abuja, a matsayin wani ɓangare na shirye-shiryen farko na ayyukan Hajji da Umrah na 2026, tare da gabatar da wannan taro gabanin ziyarar aiki ta farko da Ministan Hajji da Umrah na Saudiyya zai kawo Najeriya.

KARANTA LABARI MAKAMANCIN WANNAN: Hajjin 2026: Muhimman Ka’idojin Lafiya da Dukkan Maniyyata Dole Su Bi – NAHCON

A jawabin buɗe taron, Shugaban NAHCON, Farfesa Abdullahi Saleh Usman, ya yi maraba da tawagar Saudiyya zuwa Hajj House tare da bayyana farin cikinsa na karɓar bakuncinsu. Ya yi kira da a ƙara ƙarfafa haɗin gwiwa da fahimtar juna tsakanin NAHCON da Ma’aikatar Hajji da Umrah ta Saudiyya, tare da gabatar da buƙatar ƙarin kujerun Hajji, inda ya bayyana cewa Najeriya ta riga ta cika adadin kujerun da aka ware mata.

A yayin taron, Kwamishinan Ayyuka na NAHCON, Yarima Anofiu Elegushi, ya yi wa tawagar bayani kan matakin shirin da Najeriya ta kai dangane da Hajjin 2026. Bayanin ya haɗa da shirye-shiryen farko, tattaunawa da kamfanonin jiragen sama, tsare-tsaren masauki a Makkah da Madinah, da kuma tsarin tura bayanan alhazai kafin isowarsu. Ya jaddada cewa ba za a bari wani alhaji ya bar Najeriya ba sai an kammala dukkan takardunsa kuma an tura su aƙalla awanni 72 kafin tafiya, bisa tsauraran ƙa’idojin Saudiyya.

Manyan ƙalubalen aiki da aka tattauna sun haɗa da raguwar kujerun Hajji, matsalolin masauki, ƙarancin damar jigilar jiragen sama, da jinkirin bizar Umrah da ke shafar masu shirya tafiye-tafiye. NAHCON ta nemi ƙarin kujerun Hajji tare da roƙon sa-hannun Saudiyya kan rabon masauki da amincewar jiragen sama, sannan ta gabatar da damuwa kan matsalolin biza da ke maimaituwa. Tawagar Saudiyya ta amince za ta duba waɗannan matsaloli ta hanyoyin fasaha da suka dace.

Tawagar Saudiyya ta jaddada muhimmancin bin jadawalin Hajji na ƙasa da ƙasa ba tare da kaucewa ba, tana mai bayyana cewa shirye-shirye na wuri-wuri wajibi ne kuma ba lallai a ba da ƙarin lokaci ba. Haka kuma an bayyana sabbin buƙatun lafiya da tsaro, ciki har da bin ƙa’idojin lafiya da aka sabunta ga alhazai.

NAHCON ta kuma bayyana matakan da take ɗauka don magance matsalar wuce lokacin zama (overstay), ciki har da shirin ɗaukar bayanan biometric da kuma amfani da tsarin bin diddigin alhazai na (centralized pilgrim tracking system).

A nasa jawabin, Shugaban Cibiyar Hajji ta Najeriya (Hajj Institute of Nigeria), Farfesa Maitulare, ya yi kira da Ma’aikatar Hajji da Umrah ta Saudiyya ta ba Cibiyar cikakkiyar sahalewa, tare da ba da shawarar a yi amfani da ita wajen horas da masu kula da Hajji da kuma yaɗa sabbin manufofi da ƙa’idojin Hajji da Umrah. NAHCON ta kuma gabatar da buƙatar horas da ma’aikatanta ta tsari daga masana’antar Hajji da Umrah ta Saudiyya domin ƙara ƙarfafa ƙwarewa wajen kula da alhazai.

Dukkan ɓangarorin sun jaddada ƙudurin ci gaba da haɗin gwiwa, inda tawagar Saudiyya ta yi alƙawarin ci gaba da bayar da goyon bayan fasaha da hulɗa ta hanyoyin diflomasiyya domin magance ƙalubalen aiki, tare da tabbatar da gudanar da Hajjin 2026 cikin tsaro, sauƙi da nasara ga alhazan Najeriya, bisa hangen nesa da jagorancin NAHCON ƙarƙashin Farfesa Abdullahi Saleh Usman.

Hajin 2026 Mai'aikatar Aikin Haji ta Saudiyya NAHCON
Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp

Related Posts

NAHCON Signs 2026 Hajj Airlift Agreement, Emphasizes Compliance and Efficiency

February 25, 2026

NAHCON Ta Fayyace Batun Kujerun Hajjin 2026 da Ka’idojin Lafiya

February 24, 2026

No Additional Slots for 2026 Hajj, Says NAHCON as Visa Issuance Nears

February 24, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

Don't Miss
Nahcon

NAHCON Chairman Strengthens Ties with Saudi Embassy Ahead of 2026 Hajj

By adminFebruary 27, 20260

By Suwaiba Ahmad The Chairman/CEO of the National Hajj Commission of Nigeria (NAHCON), Ambassador Ismail…

Jigawa Pilgrims Board Seeks Smooth Immigration Process for 2026 Hajj

February 26, 2026

2026 Hajj: First Batch of Kano Pilgrims to Depart May 13

February 25, 2026

Hajj 2026: Sokoto Media Committee Urged to Ensure Smooth Information Flow

February 25, 2026
Stay In Touch
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • WhatsApp
Our Picks

NAHCON Chairman Strengthens Ties with Saudi Embassy Ahead of 2026 Hajj

February 27, 2026

Jigawa Pilgrims Board Seeks Smooth Immigration Process for 2026 Hajj

February 26, 2026

2026 Hajj: First Batch of Kano Pilgrims to Depart May 13

February 25, 2026

Hajj 2026: Sokoto Media Committee Urged to Ensure Smooth Information Flow

February 25, 2026
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
© 2026HAJJ CHRONILES

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.