Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima, ya yaba wa Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON) kan yadda ta gudanar da aikin Hajjin shekarar 2026 cikin tsari da nasara.
A cikin wata sanarwa da Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Ƙasa kan Harkokin Yaɗa Labarai da Sadarwa a Ofishin Mataimakin Shugaban Ƙasa, Stanley Nkwocha, ya sanya wa hannu, an bayyana cewa Shettima ya yi wannan yabon ne a ranar Laraba yayin da ya karɓi shugabannin Hukumar NAHCON da wakilan Hukumar Jin Daɗin Alhazai na Jihohi a ziyarar ban girma da suka kai masa a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja.
Tawagar ta ziyarci Mataimakin Shugaban Ƙasa ne domin gabatar masa da rahoto kan aikin Hajjin 2026 da aka kammala tare da bayyana shirye-shiryen da ake yi domin ayyukan Hajji na gaba.
Yayin ganawarsa da tawagar, Shettima ya yaba da ƙoƙarin da NAHCON, Hukumomin Jin Daɗin Alhazai na Jihohi da sauran masu ruwa da tsaki suka yi, tare da taya su murnar gudanar da aikin Hajjin cikin nasara ba tare da manyan matsaloli ba.
Ya ce yadda aka gudanar da Hajjin 2026 ya kamata ya zama abin koyi ga ayyukan Hajji na gaba, musamman yayin da ake shirin rungumar sabon tsarin da zai tabbatar da gudanar da Hajji cikin inganci ba tare da wata tangarɗa ba.
Tun da farko, Shugaban Hukumar NAHCON, Ambasada Ismail Abba Yusuf, ya gabatar da taƙaitaccen rahoto kan yadda aka gudanar da Hajjin 2026, inda ya kuma sanar da Mataimakin Shugaban Ƙasa game da matakin da hukumomin Saudiyya suka ɗauka na komawa tsarin gudanar da Hajji na kasuwanci tsakanin kamfanoni (Business-to-Business).
Ambasada Yusuf ya bayyana cewa matakin da hukumomin Saudiyya suka ɗauka na miƙa kula da kusan kashi 98 cikin 100 na alhazai ga kamfanonin Jirgin Yawo masu zaman kansu ya yi daidai da manufar Vision 2030 ta ƙasar Saudiyya, wadda ke ƙarfafa tsarin kasuwanci tsakanin kamfanoni.
A ƙarƙashin wannan tsari, NAHCON za ta ci gaba da aikin sa ido da tsare-tsare, yayin da za a miƙa ayyukan gudanar da Hajji ga kamfanoni masu zaman kansu.
Ya ƙara da cewa hukumar NAHCON na da cikakken ƙuduri da shirin tabbatar da nasarar aiwatar da wannan sabon tsari, yana mai cewa an riga an fara ɗaukar matakan da suka dace domin cimma wannan buri.

