Close Menu
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • Hajj News
  • Global
  • Health
  • Nahcon
  • Picture Gallery
  • Opinion
  • Videos
  • HAUSA
Facebook X (Twitter) Instagram
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram
SUBSCRIBE
  • Home
  • Hajj News

    Saudi Arabia Unveils Major Mina Expansion to Boost Pilgrim Capacity

    April 15, 2026

    Hajj Without Permit Violates Shariah Principles – Sheikh Sudais

    April 15, 2026

    Gombe Takes Lead With Early Hajj 2026 Hand Luggage and Uniform Distribution To 965 Pilgrims

    April 13, 2026

    Indonesia Moves to Curb Hajj Scams, Tighten Departure Controls Ahead of 2026 Pilgrimage

    April 13, 2026

    Pakistan Expands Hajj Facilitation with Lahore’s Inclusion in Makkah Route Initiative

    April 13, 2026
  • Global

    Indonesia Plans to Acquire Land for Hajj Village Near Makkah’s Grand Mosque

    July 31, 2025

    Egypt To Halt Land Hajj Trips by 2026 Over Saudi Transport Policy Changes

    July 31, 2025

    UAE Unveils Streamlined Hajj 2026 Accreditation Process to Ensure Transparency and Quality

    July 24, 2025

    flyadeal Aims To Serve 75,000 International Hajj Pilgrims In 2025

    January 23, 2025

    Reflections on the 4th Hajj Conference and Exhibition in Jeddah – By Muhammad Ahmad Musa

    January 21, 2025
  • Health

    Gombe Muslim Pilgrim Board Commences Vaccination for 2025 Hajj Pilgrims – By Abdulqadir Aliyu Shehu

    April 28, 2025

    NAHCON Inaugurates Committee To Review National Medical Team Guidelines for Hajj 2025

    December 19, 2024

    Saudi Health Minister Strengthen Ties With Greece On Health Cooperation During Official Visit

    November 23, 2024

    Umm Al-Qura University volunteers extend help to pilgrims in Mina during Tashreeq

    June 17, 2024

    Hajj 2024: African pilgrim airlifted for emergency care

    June 14, 2024
  • Nahcon

    NAHCON Warns Public Against Fake Hajj Visa Claims, Announces Closure of 2026 Visa Issuance

    April 15, 2026

    NAHCON Wins Reprieve: Cash PTA Approved Ahead of 2026 Hajj

    April 1, 2026

    NAHCON Chairman Felicitates Muslims on Eid-el-Fitri, Assures Improved Hajj 2026 Services

    March 19, 2026

    Senate Confirms Ismail Yusuf as NAHCON Chairman

    March 12, 2026

    NAHCON Inaugurates Central Security Committee to Safeguard 2026 Hajj Operations

    March 11, 2026
  • Picture Gallery
  • Opinion

    Gov Ahmad Aliyu and His Transformational Contributions to Hajj Administration in Sokoto

    March 23, 2026

    Nigeria Hajj Industry: Back To Square One – By Abubakar Jidda Usman

    February 11, 2026

    NAHCON Reconciliation Viewed as Positive Step for Hajj Administration – By Muhammad Sulaiman Gama

    February 2, 2026

    NAHCON Board’s Vote of No Confidence: A Mask for Self-Interest.

    February 1, 2026

    Nigeria Hajj Industry: When Would Pilgrims’ Interest Supercede Personal Interest of Handlers and Stakeholders

    January 31, 2026
  • Videos
  • HAUSA
HAJJ CHRONICLES
Home » Hukumar Alhazai ta Jihar Gombe Ta Rufe Bitar Hajjin 2025 – Daga Abdulqadir Aliyu Shehu
Hausa

Hukumar Alhazai ta Jihar Gombe Ta Rufe Bitar Hajjin 2025 – Daga Abdulqadir Aliyu Shehu

adminBy adminMay 4, 2025No Comments5 Mins Read
Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Email Telegram
IMG 20250504 WA0032

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Musulmai ta Jihar Gombe ta gudanar da bikin rufe Bitar wayar da kai da ilimantarwa na wannan shekara a ranar Lahadi, inda ta bukaci duk maniyyata da su rungumi koyarwar da suka samu yayin da suke shirin tafiya kasa Mai Tsarki.

 

A jawabinsa ga mahajjata a wajen bikin, Sakataren Hukumar Jin dadin Alhazai Alhaji Saad Hassan, ya jaddada muhimmancin bin doka da ƙa’idojin tafiye-tafiye na Hajji, musamman cikakkun takardu da katin shedar Allurar Rigakafi wato Yellow Card. Ya ce wajibi ne mahajjaci ya kasance yana dauke da takardun tafiya wato Passport da shaidar rigakafi a kowane lokaci, kasancewar hukumomin Saudiyya sun kara tsaurara matakan tantancewa a bana.

 

Alhaji Saad ya yi gargaɗi ga wadanda suka biya kuɗin Hajji ta kamfanonin masu zaman kansu da su kauracewa guraren allurar rigakafin da hukumar ke gudanarwa. Ya bayyana cewa allurar rigakafin da hukumar ke bayarwa na musamman ne kawai ga wadanda suka biya kuɗin Hajji ta hanyar hukumar Jihar Gombe ko Bankin Ja’iz.

Hukumar  Alhazai ta Jihar Gombe Ta Kaddamar da allurar Rigakafi ga Alhazan Shekarar 2025 – Daga Abdulkadir Aliyu Shehu

Ya kara da cewa hukumar za ta kara ƙaimi wajen hana mata masu juna biyu tafiya Hajji a bana, duba da abin da ya faru a shekarun baya inda wasu mata suka haihu a ƙasar Saudiyya, wanda hakan ya janyo cikas da matsaloli na lafiya da tsari. Haka kuma, ba za a bar masu fama da matsalolin lafiya masu tsanani su tafi Hajji ba.

 

Sakatare ya kuma yi kira ga ‘yan uwa da dangi da su dauki alhakin hana tura tsofaffi ko marasa lafiya zuwa kasa mai tsarki sai dai idan akwai wanda zai iya kula da su. “Idan har zai yiwu, ku biya kuɗinku tare da nasu domin ku taimaka musu a kasa mai tsarki,” in ji shi.

 

Dangane da batun Kudin Tafiye-tafiye na Hajj (BTA) Alhaji Saad ya tabbatar wa mahajjata cewa Gwamnatin Jihar Gombe tare da hukumar sun dauki matakan da suka dace don ganin an guje wa irin matsalolin da suka faru a shekarar 2024, inda Babban Bankin Najeriya ya kasa cika alkawarin bayar da dala 500, inda aka bai wa mahajjata dala 400 kacal.

 

Domin gyara hakan, ya bayyana cewa Gwamnatin Jihar Gombe ta dauki nauyin ganin kowanne mahajjaci ya samu cikakken dala 500 a bana. Haka kuma, Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ya amince da bayar da goron Sallah ta musamman har Riyal 200 ga kowanne mahajjaci, tare da shirin samar da abinci na musamman a lokacin zama a Arafat.

 

Alhaji Saad ya kuma bukaci mahajjata da su biya kuɗin Hadaya (layya) ta hannun jami’an Hajji na ƙananan hukumominsu, ko ta ofishin hukumar a Gombe, ko kuma ta bankin Ja’iz, domin tabbatar da tsari da kare mahajjata daga fadawa hannun masu damfara.

 

A nasa jawabin, Shugaban Hukumar kuma Sarkin Dukku, Mai Martaba Alhaji Abdulkadir Haruna Rasheed, ya yi godiya ga Allah Madaukakin Sarki bisa nasarar kammala shirin horar da mahajjata na bana cikin nasara. Ya mika godiyarsa ta musamman ga Gwamna Inuwa Yahaya saboda goyon bayan da ya bayar, musamman wajen samar da masaukai masu kyau kusa da Harami a Makkah, wanda ya ce ya zama ɗaya daga cikin mafiya inganci ga mahajjatan Najeriya.

 

Sarkin ya ce mataki na gaba shi ne hukumar ta tabbatar da aiwatar da duk shirye-shiryen da suka tsara don ganin an samu nasarar gudanar da aikin Hajjin 2025. Ya nuna kwarin gwiwa cewa mahajjatan Jihar Gombe za su kasance masu biyayya da ladabi a cikin gida da wajen ƙasa.

 

Ya kuma shawarci mahajjata da su kiyaye kuɗin BTA da aka ba su, yana mai gargadi cewa hukumar ba za ta iya maidawa ko biya wani da ya rasa kuɗinsa ba. “Zama a Saudiyya ba tare da kudi ba abu ne mai matuƙar wahala,” in ji shi.

 

Sarkin ya kuma ja kunnen mahajjata kan bada aron katin shaida ko kayan da aka raba musu daga hukumar anan Gombe ko wanda hukumomin Saudiyya zasu basu. Ya umurci mahajjata da su rika sanya su a wuyansu a kowane lokaci domin sauƙin tantancewa da kare kansu daga matsala a ƙasar.

 

A tunda farko a nasa Jawabin, Shugaban Sashen Horo da Wayar da Kai na Hukumar, Malam Maiwada Dahiru, ya yabawa Sarkin Dukku da Sakatare hukumar saboda cikakken goyon bayan da suka bayar. Ya bayyana godiyarsa musamman irin hadin kai da goyin baya da aka basu da damar da gudanar da shirin BITA a fadin jihar cikin sauki.

 

Malam Dahiru ya bukaci mahajjata da su aiwatar da duk darussan da suka koya a shirin, yana mai jaddada cewa ilimi da ladabi su ne ginshiƙai wajen samun Hajji mai karɓuwa da lada.

 

Wadanda suka halarci bikin sun hada da manyan jami’an hukumar, mambobin kwamitin gudanarwa, Shugaban Kamfanin Kautal Jude Travel and Tours, da wasu muhimman masu ruwa da tsaki da suka taka rawa wajen nasarar shirin.

 

Bikin ya zama wata muhimmiyar alama ta cika wani muhimmin mataki a shirin tafiya Hajjin 2025, inda Jihar Gombe ta sake nuna aniyarta na tabbatar da lafiya, jin daɗi, da cikar biyan buƙatun ruhin mahajjatanta a wannan tafiya mai tsarki.

Bitar Alhazai Gombe Hajj 2025 Hukumar Alhazai
Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp

Related Posts

2026 Hajj: Gombe Ta Cimma Muhimmin Nasara Yayin da Aka Fara Feshin Maganin Kwari a Sansanin Alhazai

April 16, 2026

Za A Ciyar Da Alhazan Jahar Jigawa Abinci Sau 3 A Rana Yayin Aikin Hajin 2026

April 16, 2026

2026 Hajj: Gombe Records Milestone as Camp Fumigation Gets Underway – By Abdulkadir Aliyu

April 16, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

Don't Miss
Uncategorized

Bauchi Begins Distribution of Hajj Uniforms, Travel Bags to 2026 Pilgrims

By adminApril 16, 20260

Flagging off the exercise at the Board’s premises, the Executive Secretary, Dr. Imam Abdurrahman Ibrahim…

2026 Hajj: Gombe Ta Cimma Muhimmin Nasara Yayin da Aka Fara Feshin Maganin Kwari a Sansanin Alhazai

April 16, 2026

Za A Ciyar Da Alhazan Jahar Jigawa Abinci Sau 3 A Rana Yayin Aikin Hajin 2026

April 16, 2026

Jigawa Pilgrims to Enjoy Full Feeding Package for 2026 Hajj

April 16, 2026
Stay In Touch
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • WhatsApp
Our Picks

Bauchi Begins Distribution of Hajj Uniforms, Travel Bags to 2026 Pilgrims

April 16, 2026

2026 Hajj: Gombe Ta Cimma Muhimmin Nasara Yayin da Aka Fara Feshin Maganin Kwari a Sansanin Alhazai

April 16, 2026

Za A Ciyar Da Alhazan Jahar Jigawa Abinci Sau 3 A Rana Yayin Aikin Hajin 2026

April 16, 2026

Jigawa Pilgrims to Enjoy Full Feeding Package for 2026 Hajj

April 16, 2026
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
© 2026HAJJ CHRONILES

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.