Close Menu
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • Hajj News
  • Global
  • Health
  • Nahcon
  • Picture Gallery
  • Opinion
  • Videos
  • HAUSA
Facebook X (Twitter) Instagram
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram
SUBSCRIBE
  • Home
  • Hajj News

    1,357 Pakistani Pilgrims Arrive in Madinah as Hajj 2026 Airlift Commences

    April 20, 2026

    Hajj 2026: Saudi Arabia Plans Massive Airlift with 12,000+ Flights for Pilgrims

    April 20, 2026

    Hajj 2026: Health Workers Invited to Join Volunteer Programme

    April 17, 2026

    Saudi Arabia Unveils Major Mina Expansion to Boost Pilgrim Capacity

    April 15, 2026

    Hajj Without Permit Violates Shariah Principles – Sheikh Sudais

    April 15, 2026
  • Global

    Indonesia Plans to Acquire Land for Hajj Village Near Makkah’s Grand Mosque

    July 31, 2025

    Egypt To Halt Land Hajj Trips by 2026 Over Saudi Transport Policy Changes

    July 31, 2025

    UAE Unveils Streamlined Hajj 2026 Accreditation Process to Ensure Transparency and Quality

    July 24, 2025

    flyadeal Aims To Serve 75,000 International Hajj Pilgrims In 2025

    January 23, 2025

    Reflections on the 4th Hajj Conference and Exhibition in Jeddah – By Muhammad Ahmad Musa

    January 21, 2025
  • Health

    Gombe Commences Vaccination of 965 Pilgrims Ahead of 2026 Hajj- By Abdulkadir Aliyu

    April 25, 2026

    Gombe Muslim Pilgrim Board Commences Vaccination for 2025 Hajj Pilgrims – By Abdulqadir Aliyu Shehu

    April 28, 2025

    NAHCON Inaugurates Committee To Review National Medical Team Guidelines for Hajj 2025

    December 19, 2024

    Saudi Health Minister Strengthen Ties With Greece On Health Cooperation During Official Visit

    November 23, 2024

    Umm Al-Qura University volunteers extend help to pilgrims in Mina during Tashreeq

    June 17, 2024
  • Nahcon

    FG Weighs Policy Options to Cushion Aviation Fuel Costs, Assures Seamless 2026 Hajj Airlift

    April 30, 2026

    Hajj 2026: Inaugural Flight to Takeoff 3rd May – NAHCON

    April 28, 2026

    Kogi Clerics Hail NAHCON Chairman, Seek Sectoral Reforms

    April 26, 2026

    NAHCON Inaugurates Media Team for Hajj 2026, Urges Professionalism and Collaboration

    April 21, 2026

    NAHCON Warns Public Against Fake Hajj Visa Claims, Announces Closure of 2026 Visa Issuance

    April 15, 2026
  • Picture Gallery
  • Opinion

    Gov Ahmad Aliyu and His Transformational Contributions to Hajj Administration in Sokoto

    March 23, 2026

    Nigeria Hajj Industry: Back To Square One – By Abubakar Jidda Usman

    February 11, 2026

    NAHCON Reconciliation Viewed as Positive Step for Hajj Administration – By Muhammad Sulaiman Gama

    February 2, 2026

    NAHCON Board’s Vote of No Confidence: A Mask for Self-Interest.

    February 1, 2026

    Nigeria Hajj Industry: When Would Pilgrims’ Interest Supercede Personal Interest of Handlers and Stakeholders

    January 31, 2026
  • Videos
  • HAUSA
HAJJ CHRONICLES
Home » Jihar Legas Ta Kafa Kwamitin Wucin Gadi na Hajjin 2026, Za a Fara Jirgin Farko Ranar 7 ga Mayu
Hausa

Jihar Legas Ta Kafa Kwamitin Wucin Gadi na Hajjin 2026, Za a Fara Jirgin Farko Ranar 7 ga Mayu

adminBy adminApril 30, 2026No Comments3 Mins Read
Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Email Telegram
Shugaban Kasar Guinea Bissau Ya Karrama Gwamna Abba Kabir Yusuf Da Babbar L 20260430 001555 0000

Gwamnatin Jihar Legas ta kafa wani kwamitin wucin gadi domin shirye-shiryen gudanar da aikin Hajjin shekarar 2026 a ƙasar Saudiyya.

 

A sanarwar da Daraktan Hulda da jama’a na Hukumar, Taofeek Lawal ya fitar, yace an ƙaddamar da kwamitin, wanda Mai Bai wa Gwamna Shawara kan Harkokin Addinin Musulunci, Dr. Ahmad Abdullahi Jebe ke jagoranta ne ta hannun Kwamishinan Harkokin Gida, Olanrewaju Ibrahim Layode, a sakatariyar gwamnati da ke Alausa, Ikeja, a ranar Laraba.

 

Da yake jawabi ga mambobin kwamitin, Layode ya bayyana cewa an naɗa su ne bisa la’akari da ƙwarewarsu da jajircewarsu, domin tabbatar da ingantaccen tsari, daidaitawa da kuma gudanar da ayyukan da suka shafi Hajjin 2026 cikin nasara.

 

Ya buƙace su da su gudanar da ayyukansu da cikakken ƙwazo, gaskiya da riƙon amana, bisa manufofin Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Musulmi ta Jihar Legas.
A cewarsa, aikin kwamitin ya haɗa da bayar da gudummawa a fannoni kamar daidaita harkokin sufuri da kayan aiki, kula da jin daɗin maniyyata, masauki, shirye-shiryen lafiya, da sauran ayyukan da za a iya ɗora musu lokaci zuwa lokaci.

 

Yayin da yake taya su murna, ya jaddada cewa naɗin nasu ya fara aiki nan take kuma zai ci gaba har zuwa ƙarshen aikin Hajjin 2026.

 

Da yake mayar da jawabi a madadin sauran mambobi, shugaban kwamitin, Dr. Ahmad Jebe, ya gode wa Gwamna, Babajide Olusola Sanwo-Olu; Mataimakin Gwamna, Kadiri Obafemi Hamzat; da kuma Kwamishinan Harkokin Gida, bisa ba su wannan dama ta yi wa jihar hidima.

 

Ya tabbatar da cewa za su mutunta amanar da aka ɗora musu, tare da alƙawarin yin aiki tukuru domin ganin an samu nasarar gudanar da aikin Hajjin. Haka kuma ya roƙi a ba su cikakken goyon baya domin sauƙaƙa aikin da ke gabansu.

 

Daga nan ya sanar da rabon ƙananan kwamitoci da shugabanninsu kamar haka: Masauki (Hon. Musliudeen Maiyegun); Jin Daɗi (Malam Ajisegiri Ismail Ajibade); Manifet, Biza da Yaɗa Labarai (Hon. Waheed Lolade Shonibare); Madina/Mina da Arafat (Engr. Shakiru Ayinde Gafar).

 

Sauran sun haɗa da Wa’azi/Wayar da Kai (Farfesa Kabir Paramole); Sufuri (Alhaji Mojeed Sanni) da Kwamitin Kayan Jaka da Auna Nauyi (Alhaji Yusuf Ara).

 

A halin yanzu, Hon. Layode ya bayyana cewa jigilar maniyyata 1,600 na Jihar Legas za ta fara ne a ranar Alhamis, 7 ga Mayu, da jirgi na farko mai ɗauke da maniyyata 345.

 

A cewarsa, za a ci gaba da jigilar kamar haka: jirgi na biyu ranar Juma’a 8 ga Mayu; na uku ranar Lahadi 10 ga Mayu; na huɗu ranar Talata 12 ga Mayu; yayin da jirgi na ƙarshe zai tashi ranar Laraba 13 ga Mayu, 2026. Ya ce an tsara hakan ne bisa jadawalin da National Hajj Commission of Nigeria ta fitar.

 

Haka kuma ya sanar da kwamitin cewa kamfanin jirgin sama na Flynas, wanda NAHCON ta zaɓa domin jigilar maniyyatan jihar, ya amince da ƙara nauyin kaya daga kilogiram 32 zuwa 46. Ya ƙara da cewa kowanne maniyyaci zai samu jakunkuna biyu masu nauyin kilogiram 23 kowanne domin manyan kaya, yayin da kayan hannu zai ci gaba da kasancewa kilogiram 8.

2026 Hajj Jihar Legas Jirgin farko Kwamiti
Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp

Related Posts

Lagos constitutes ad-hoc committee for 2026 Hajj, begins airlifting May 7

April 30, 2026

Jirgin Farko na Aikin Hajjin 2026 Zai Tashi Ranar 3 ga Mayu – NAHCON

April 28, 2026

NAHCON Ta Tattauna da Malaman Najeriya Kan Ilimantar da Alhazai da Shiryar da Su Ta Fuskar Addini Gabanin Aikin Hajji

April 26, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

Don't Miss
Nahcon

FG Weighs Policy Options to Cushion Aviation Fuel Costs, Assures Seamless 2026 Hajj Airlift

By adminApril 30, 20260

By Fatima Sanda Usara The Chairman of the National Hajj Commission of Nigeria, Ambassador Ismail…

Saudi Red Crescent Saves Indonesian Pilgrim After Cardiac Arrest in Madinah

April 30, 2026

Saudi Arabia Approves 10–15 Days Paid Hajj Leave for Eligible Workers

April 30, 2026

Jihar Legas Ta Kafa Kwamitin Wucin Gadi na Hajjin 2026, Za a Fara Jirgin Farko Ranar 7 ga Mayu

April 30, 2026
Stay In Touch
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • WhatsApp
Our Picks

FG Weighs Policy Options to Cushion Aviation Fuel Costs, Assures Seamless 2026 Hajj Airlift

April 30, 2026

Saudi Red Crescent Saves Indonesian Pilgrim After Cardiac Arrest in Madinah

April 30, 2026

Saudi Arabia Approves 10–15 Days Paid Hajj Leave for Eligible Workers

April 30, 2026

Jihar Legas Ta Kafa Kwamitin Wucin Gadi na Hajjin 2026, Za a Fara Jirgin Farko Ranar 7 ga Mayu

April 30, 2026
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
© 2026HAJJ CHRONILES

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.