Close Menu
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • Hajj News
  • Global
  • Health
  • Nahcon
  • Picture Gallery
  • Opinion
  • Videos
  • HAUSA
Facebook X (Twitter) Instagram
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram
SUBSCRIBE
  • Home
  • Hajj News

    2026/1447 Hajj Preparations Officially Launched as NAHCON Joins Global Pilgrimage Community in Closing Ceremony

    June 9, 2025

    No Lives Lost in Makkah Fire, Senate Foreign Affairs Committee Confirms

    June 9, 2025

    Pilgrimage and Leadership: How Governor Inuwa Yahaya Stood Tall Among His Peers During the 2025 Hajj – Abdulkadir Aliyu Shehu

    June 8, 2025

    From Crisis to Victory: NAHCON Chairman Called to Prostrate in Thanks for 2025 Hajj Breakthrough – By Shamwil Isah

    June 8, 2025

    Governor Abba Yusuf Disburses ₦361 Million Support to Kano Pilgrims in Mina

    June 8, 2025
  • Global

    flyadeal Aims To Serve 75,000 International Hajj Pilgrims In 2025

    January 23, 2025

    Reflections on the 4th Hajj Conference and Exhibition in Jeddah – By Muhammad Ahmad Musa

    January 21, 2025

    Hajj and Umrah Expo 2025: Innovation and Collaboration Take Center Stage in Jeddah – By Fatima Sanda Usara

    January 14, 2025

    Makkah Red Crescent Boosts Preparedness to Heavy Rainfall

    January 6, 2025

    Intense Rainfall Sweeps Through Makkah, Madina and Jeddah

    January 6, 2025
  • Health

    Gombe Muslim Pilgrim Board Commences Vaccination for 2025 Hajj Pilgrims – By Abdulqadir Aliyu Shehu

    April 28, 2025

    NAHCON Inaugurates Committee To Review National Medical Team Guidelines for Hajj 2025

    December 19, 2024

    Saudi Health Minister Strengthen Ties With Greece On Health Cooperation During Official Visit

    November 23, 2024

    Umm Al-Qura University volunteers extend help to pilgrims in Mina during Tashreeq

    June 17, 2024

    Hajj 2024: African pilgrim airlifted for emergency care

    June 14, 2024
  • Nahcon

    NAHCON Chairman Attributes 2025 Hajj Success to Divine Blessings, Pledges Greater Efforts for 2026

    July 10, 2025

    The 2026 Hajj Countdown Has Begun: Why Early Compliance and Payment Is Crucial

    July 3, 2025

    NAHCON Concludes 2025 Hajj Return Operations as Last Flight Departs for Kaduna

    July 2, 2025

    Update on Nigeria’s 2025 Airlift

    July 1, 2025

    NAHCON Provides Update on Return Airlift, Cites July 2 as New Target Date

    June 26, 2025
  • Picture Gallery
  • Opinion

    NAHCON: The Journey so Far, Under Professor Abdullahi Saleh Usman(Part 1)

    July 11, 2025

    Who’s Trying to Undermine NAHCON’s Progress?

    June 25, 2025

    Professor Abdullahi Saleh and Pilgrims Spiritual Reawakening – Dr Usman Ahmad Mustapha

    June 15, 2025

    This is Ismail Shuaibu Musa — and this is his story – By Fatima Sanda Usara

    June 5, 2025

    Exposing Leadership Newspaper’s many lies against NAHCON chairman – By Ahmad Shafi’i PhD

    May 8, 2025
  • Videos
  • HAUSA
HAJJ CHRONICLES
Home » Shugaban NAHCON Ya Bukaci Gaggauta Rijistar Hajjin 2026, Ya Danganta Nasarar 2025 da Albarkar Ubangiji
Hausa

Shugaban NAHCON Ya Bukaci Gaggauta Rijistar Hajjin 2026, Ya Danganta Nasarar 2025 da Albarkar Ubangiji

adminBy adminJuly 11, 2025No Comments3 Mins Read
Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Email Telegram
IMG 20250710 231118

Shugaban Hukumar JAlhazai ta Najeriya (NAHCON), Farfesa Abdullahi Saleh Usman, ya bayyana godiya ta musamman ga Allah Madaukakin Sarki bisa nasarar gudanar da aikin Hajjin 2025, yana mai cewa nasarar ta samo asali ne daga albarkar Allah da hadin kan dukkan masu ruwa da tsaki.

KARANTA LABARI MAKAMANCIN WANNAN: Gwamnatin Tarayya Ta Yabawa Shugaban NAHCON Bisa Kokarin Inganta Jin Dadin Alhazai- Daga Nura Ahmad Dakata

Farfesa Saleh ya bayyana haka ne yayin da yake zantawa da manema labarai a Kano, jim kadan bayan dawowarsa daga kasa mai tsarki inda aka kammala aikin Hajjin bana.

 

A cewarsa, nasarar da aka samu ba tasa kadai bace, ko ta hukumar NAHCON, sai dai wata baiwa ce daga Allah wanda Ya sa aikin ya tafi lafiya kuma cikin nasara.

 

“Nasararmu a wannan shekarar ta Hajji ta samu ne da yardar Allah. Ba tawa bace, ba kuma ta hukumar NAHCON kadai ba Allah ne Ya albarkaci wannan aiki, Ya shiryar da mu duka cikin hanya madaidaiciya,” in ji shi.

 

Ya yaba da hadin kai da halin kirki da alhazan Najeriya suka nuna, tare da jinjinawa gudunmuwar da sauran bangarori suka bayar, ciki har da kwamitocin Majalisar Dattawa da ta Wakilai masu kula da harkokin Hajji.

 

“Kun ji komai daga bakin shugabanninmu daga kwamitocin Majalisa. Sun wakilce ni kuma sun bayyana abinda ke cikin zuciyata. Ina kuma matukar godiya ga kafafen yada labarai bisa kokarinku na isar da sakonmu ga jama’a. Muna godiya da hadin kai da sadaukarwarku,” ya kara da cewa.

 

Shugaban NAHCON ya jinjina wa goyon bayan da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da mataimakinsa Kashim Shettima suka baiwa hukumar, yana mai cewa irin wannan goyon baya ne ya taimaka wajen nasarar gudanar da aikin Hajjin bana.

 

“Muna godiya matuka ga Gwamnatin Tarayya. Shugaba Tinubu ya bamu cikakken goyon baya. Mataimakin Shugaba Shettima wanda mukewa aiki a ofishinsa, yana bin diddigin abubuwan da muke yi yana tambaya yau me ke faruwa, gobe me za ku yi. Wannan kulawa tasa muka yi aiki kamar iyali daya, muna da hadin kai da girmama juna,” in ji shi.

 

Yayin da ake shirin Hajjin shekarar 2026, Farfesa Saleh ya tabbatar da cewa NAHCON ta koyi darussa da dama daga aikin bana, kuma tana shirye fiye da da.

 

“InshaAllah, da irin kwarewar da muka samu da darussan da muka koya a bana, mun shirya sosai don gudanar da aikin Hajjin shekara mai zuwa. Muna rokon Allah Madaukakin Sarki Ya sanya Hajjin 2026 ya fi na bana nasara da albarka,” ya kammala.

Farfesa Abdullahi Saleh Hajin 2026 Shugaban NAHCON
Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp

Related Posts

Kidayar Lokacin Aikin Hajjin 2026 Ya Fara: Dalilin Da Yasa Cika Ka’idoji Da Biyan Kudin Hajji Tun Da Wuri Yake Da Muhimmanci – Daga Sani Muhammed Shafi’i

July 3, 2025

NAHCON Ta Fitar da Sabon Jadawalin Dawowar Maniyyata, Ta Sanya Ranar 2 ga Yuli a Matsayin Sabuwar Rana

June 26, 2025

NAHCON Na Tabbatar da Ciyar da Maniyyatan Najeriya Sama da 17,000 Ingantaccen abinci a Madinah – Daga Ahmad Muazu

May 16, 2025
Leave A Reply Cancel Reply

Don't Miss
Opinion

NAHCON: The Journey so Far, Under Professor Abdullahi Saleh Usman(Part 1)

By adminJuly 11, 20250

By :Ibrahim Abubakar Nagarta In retrospect, the National hajj Commission of Nigeria (NAHCON) got…

Shugaban NAHCON Ya Bukaci Gaggauta Rijistar Hajjin 2026, Ya Danganta Nasarar 2025 da Albarkar Ubangiji

July 11, 2025

NAHCON Chairman Attributes 2025 Hajj Success to Divine Blessings, Pledges Greater Efforts for 2026

July 10, 2025

Mass Deportation: 8,000+ Illegal Migrants Sent Home from Saudi Arabia in Seven Days

July 8, 2025
Stay In Touch
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • WhatsApp
Our Picks

NAHCON: The Journey so Far, Under Professor Abdullahi Saleh Usman(Part 1)

July 11, 2025

Shugaban NAHCON Ya Bukaci Gaggauta Rijistar Hajjin 2026, Ya Danganta Nasarar 2025 da Albarkar Ubangiji

July 11, 2025

NAHCON Chairman Attributes 2025 Hajj Success to Divine Blessings, Pledges Greater Efforts for 2026

July 10, 2025

Mass Deportation: 8,000+ Illegal Migrants Sent Home from Saudi Arabia in Seven Days

July 8, 2025
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
© 2025HAJJ CHRONILES

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.