Close Menu
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • Hajj News
  • Global
  • Health
  • Nahcon
  • Picture Gallery
  • Opinion
  • Videos
  • HAUSA
Facebook X (Twitter) Instagram
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram
SUBSCRIBE
  • Home
  • Hajj News

    2026/1447 Hajj Preparations Officially Launched as NAHCON Joins Global Pilgrimage Community in Closing Ceremony

    June 9, 2025

    No Lives Lost in Makkah Fire, Senate Foreign Affairs Committee Confirms

    June 9, 2025

    Pilgrimage and Leadership: How Governor Inuwa Yahaya Stood Tall Among His Peers During the 2025 Hajj – Abdulkadir Aliyu Shehu

    June 8, 2025

    From Crisis to Victory: NAHCON Chairman Called to Prostrate in Thanks for 2025 Hajj Breakthrough – By Shamwil Isah

    June 8, 2025

    Governor Abba Yusuf Disburses ₦361 Million Support to Kano Pilgrims in Mina

    June 8, 2025
  • Global

    Indonesia Plans to Acquire Land for Hajj Village Near Makkah’s Grand Mosque

    July 31, 2025

    Egypt To Halt Land Hajj Trips by 2026 Over Saudi Transport Policy Changes

    July 31, 2025

    UAE Unveils Streamlined Hajj 2026 Accreditation Process to Ensure Transparency and Quality

    July 24, 2025

    flyadeal Aims To Serve 75,000 International Hajj Pilgrims In 2025

    January 23, 2025

    Reflections on the 4th Hajj Conference and Exhibition in Jeddah – By Muhammad Ahmad Musa

    January 21, 2025
  • Health

    Gombe Muslim Pilgrim Board Commences Vaccination for 2025 Hajj Pilgrims – By Abdulqadir Aliyu Shehu

    April 28, 2025

    NAHCON Inaugurates Committee To Review National Medical Team Guidelines for Hajj 2025

    December 19, 2024

    Saudi Health Minister Strengthen Ties With Greece On Health Cooperation During Official Visit

    November 23, 2024

    Umm Al-Qura University volunteers extend help to pilgrims in Mina during Tashreeq

    June 17, 2024

    Hajj 2024: African pilgrim airlifted for emergency care

    June 14, 2024
  • Nahcon

    NAHCON Chairman Strengthens Ties with Saudi Embassy Ahead of 2026 Hajj

    February 27, 2026

    NAHCON Signs 2026 Hajj Airlift Agreement, Emphasizes Compliance and Efficiency

    February 25, 2026

    No Additional Slots for 2026 Hajj, Says NAHCON as Visa Issuance Nears

    February 24, 2026

    NAHCON Unveils Reforms, Clarifies Quota Adjustment Ahead of 2026 Hajj – By Abdulbasit Abba

    February 23, 2026

    NAHCON Raises Alarm Over Fake Facebook Account Impersonating Chairman

    February 22, 2026
  • Picture Gallery
  • Opinion

    Nigeria Hajj Industry: Back To Square One – By Abubakar Jidda Usman

    February 11, 2026

    NAHCON Reconciliation Viewed as Positive Step for Hajj Administration – By Muhammad Sulaiman Gama

    February 2, 2026

    NAHCON Board’s Vote of No Confidence: A Mask for Self-Interest.

    February 1, 2026

    Nigeria Hajj Industry: When Would Pilgrims’ Interest Supercede Personal Interest of Handlers and Stakeholders

    January 31, 2026

    Who Is Afraid of Pakistan? By Faruku Umar

    January 31, 2026
  • Videos
  • HAUSA
HAJJ CHRONICLES
Home » Labari Da Dumiduminsa: Shugaba Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Duba Rage Kudin Hajin 2026
Hausa

Labari Da Dumiduminsa: Shugaba Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Duba Rage Kudin Hajin 2026

adminBy adminOctober 6, 2025No Comments3 Mins Read
Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Email Telegram
FB IMG 1758040218616

Shugaban Ƙasa ya umarci Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON) da ta fitar da sabon farashi cikin kwanaki biyu.

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima, ne ya isar da umarnin Shugaban Ƙasa yayin wani taro da ya gudana da shugabannin hukumar NAHCON a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja, a ranar Litinin.

Ya bukaci a samu haɗin kai tsakanin jami’an ƙasa da na jihohi, ciki har da gwamnonin jihohi, wajen tsara da kuma amincewa da sabon tsarin farashin aikin Hajjin.

Haka kuma, ya jaddada bukatar daukar matakin gaggawa daga dukkan masu ruwa da tsaki don tabbatar da biyan kuɗaɗe cikin lokaci da aika su zuwa Babban Bankin Najeriya (CBN), domin gudanar da aikin Hajji ba tare da tangarda ba.

Yayin da yake amsa tambayoyi daga manema labarai bayan kammala taron da Mataimakin Shugaban Ƙasa, Mataimakin Shugaban Ma’aikata na Fadar Shugaban Ƙasa, Sanata Ibrahim Hadejia, ya bayyana cewa taron ya gudana ne domin kammala shirye-shiryen aikin Hajjin 2026, musamman wajen tantance farashin aikin.

Ya bayyana cewa manufar gwamnati ita ce rage nauyin kuɗin da maniyyata za su biya, duba da halin tattalin arzikin ƙasa da sauye-sauyen da ake aiwatarwa a wannan lokaci.

Ya ce, “Farashin musayar kuɗi na ƙasa da ƙasa yana ci gaba da ingantuwa, kuma darajar naira tana ƙaruwa sakamakon gyare-gyaren tattalin arzikin da gwamnati ke aiwatarwa. Mataimakin Shugaban Ƙasa ya lura cewa idan maniyyata sun biya tsakanin Naira miliyan 8.5 zuwa 8.6 bisa ga tsohon farashin musayar kuɗi, yanzu da naira ta ƙara ƙarfi, to ya dace a rage kuɗin aikin, domin maniyyata su amfana da sauyin.”

“Don haka, hukumar NAHCON da jami’anta sun samu umarni da su koma su sake nazari bisa sabon farashin musayar kuɗi. Idan muka cimma abin da muke fata, za a samu gagarumin sauƙin kuɗin aikin Hajji.”

A nasa bangaren, Sakataren Hukumar Alhazai ta Ƙasa, Dokta Mustapha Muhammad, ya bayyana cewa umarnin Shugaban Ƙasa zai ƙara yawan maniyyatan da za su yi aikin Hajji a bana.

“Wannan ci gaba ne mai kyau, domin idan an rage kuɗin aikin Hajji, zai fi sauƙi ga musulmai da dama da ke da niyyar zuwa. Saboda haka, kamar yadda Mataimakin Shugaban Ƙasa ya umurce mu, za mu yi aiki tukuru daga yau zuwa gobe don ganin mun rage farashin zuwa mafi ƙaranci, domin kowa da kowa ya samu damar aiwatar da wannan muhimmin rukuni na addinin Musulunci.”

Haka kuma, Shugaban Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kebbi, wanda kuma shi ne Mataimakin Shugaban Kungiyar Shugabannin Hukumar Alhazai na Jihohi 36 da Babban Birnin Tarayya, Alhaji Faruk Aliyu Yaro, ya nuna farin ciki da wannan umarni daga shugaban ƙasa.

Ya ce, “Muna matuƙar farin ciki saboda Shugaban Ƙasa da Mataimakin Shugaban Ƙasa sun riga sun shiga tsakani. Muna gode wa Allah bisa wannan mataki, wanda ake sa ran zai rage farashin aikin Hajji. Don haka muna farin ciki ƙwarai.”

(Daily Trust)

Hajin 2026 Kudin Haji Shugaba Tinubu
Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp

Related Posts

NAHCON Ta Fayyace Batun Kujerun Hajjin 2026 da Ka’idojin Lafiya

February 24, 2026

Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Nemi Ƙarfafa Haɗin Gwiwa Da FAAN Da Kwastam Gabanin Ayyukan Hajji

February 16, 2026

Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Kaddamar Da Bitar Alhazai Ta Kafar Rediyo

February 15, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

Don't Miss
Nahcon

NAHCON Chairman Strengthens Ties with Saudi Embassy Ahead of 2026 Hajj

By adminFebruary 27, 20260

By Suwaiba Ahmad The Chairman/CEO of the National Hajj Commission of Nigeria (NAHCON), Ambassador Ismail…

Jigawa Pilgrims Board Seeks Smooth Immigration Process for 2026 Hajj

February 26, 2026

2026 Hajj: First Batch of Kano Pilgrims to Depart May 13

February 25, 2026

Hajj 2026: Sokoto Media Committee Urged to Ensure Smooth Information Flow

February 25, 2026
Stay In Touch
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • WhatsApp
Our Picks

NAHCON Chairman Strengthens Ties with Saudi Embassy Ahead of 2026 Hajj

February 27, 2026

Jigawa Pilgrims Board Seeks Smooth Immigration Process for 2026 Hajj

February 26, 2026

2026 Hajj: First Batch of Kano Pilgrims to Depart May 13

February 25, 2026

Hajj 2026: Sokoto Media Committee Urged to Ensure Smooth Information Flow

February 25, 2026
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
© 2026HAJJ CHRONILES

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.