Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Bauchi ta sanar da jadawalin jigilar maniyyata na shekarar 2026, yayin da shirye-shirye ke ƙara ƙarfi domin gudanar da aikin Hajjin.
A sanarwar da Jami’in hulda da jama’a na Hukumar, Mohd Nasir Bala ya fitar, yace Sakataren zartarwa na hukumar, Dakta Imam Abdurrahman Ibrahim Idris, ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai da aka gudanar a ofishinsa, inda ya yi bayani kan muhimman sabbin abubuwa da suka shafi aikin Hajjin mai zuwa.
Dakta Idris ya bayyana cewa waɗanda sunayensu ba su bayyana a jerin ƙarshe ba suna da zaɓuɓɓuka guda biyu: ko dai su mayar da kuɗinsu zuwa Hajjin shekara mai zuwa ko kuma su nemi a dawo musu da kuɗinsu daga hukumar.
Ya ƙara da cewa wannan lamari bai faru sakamakon kuskuren hukumar ba, sai dai ya samo asali ne daga umarnin Hukumar Alhazai ta kasa wanda ta rage yawan kujerun Hajji da aka ware wa Najeriya. A cewarsa, an rage kujeru daga 95,000 zuwa 41,000, lamarin da ya shafi maniyyata da dama a faɗin ƙasar.
Ya bayyana cewa wannan ragi wani ɓangare ne na tsarin gyara na duniya da ya shafi ƙasashe da dama, inda ya buƙaci maniyyata su tabbatar sun duba sunayensu a jerin da aka amince da shi.
Dakta Idris ya roƙi waɗanda abin ya shafa da su yi haƙuri tare da fahimta, yana mai tabbatar da cewa hukumar na aiki da gaskiya da adalci.
Haka kuma, ya sanar da cewa za a fara rabon kayan sawa da jakunkunan tafiya ga waɗanda aka yi nasara daga ranar Alhamis, 16 ga Afrilu, 2026.
Ya kuma bayyana cewa a halin yanzu Jihar Bauchi na da maniyyata 2,086 da suka yi rijista domin aikin Hajjin 2026.
Daga ƙarshe, ya jaddada muhimmancin bin sabbin ƙa’idojin da hukumomin Saudiyya suka kafa, yana mai gargadin cewa dole ne maniyyata su kiyaye duk dokoki yayin gudanar da aikin Hajjin.
Ya shawarci maniyyata da su rika bibiyar bayanai ta hanyoyin sadarwa na hukuma kamar rediyo, kafafen sada zumunta da kuma ofisoshin Hajji na ƙananan hukumomi domin samun sabbin bayanai cikin lokaci.

