Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta buƙaci dukkan maniyyatan da suka yi rajista domin gudanar da aikin Hajjin shekarar 2027 da su miƙa ingantattun fasfo ga Hukumar daga ranar Litinin, 3 ga Agusta, zuwa Juma’a, 7 ga Agusta, 2026.
Jami’in Hulɗa da Jama’a na Hukumar, Sulaiman Abdullahi Dederi, ya bayyana cewa Darakta Janar na Hukumar, Abubakar Ibrahim Matawalle, ne ya sanar da hakan yayin wata ganawa da manema labarai a ranar Litinin.
A cewar Darakta Janar ɗin, miƙa fasfo da wuri yana da matuƙar muhimmanci domin bai wa Hukumar damar fara tattara takardun da ake buƙata da kuma kammala sauran shirye-shiryen gudanarwa gabanin aikin Hajjin shekarar 2027.
Ya ƙara da cewa wannan mataki zai taimaka wajen kammala sarrafa takardun tafiya cikin lokaci tare da cika dukkan wa’adin da hukumomin da abin ya shafa suka gindaya, domin tabbatar da gudanar da aikin Hajji cikin sauƙi da nasara.
Matawalle ya kuma yi kira ga dukkan maniyyatan da suka yi rajista da su bi wannan umarni ta hanyar miƙa fasfofinsu cikin wa’adin da aka kayyade, domin kauce wa jinkiri wajen kammala takardun da suka shafi tafiyarsu ta Hajji.
Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano tana godiya ga dukkan maniyyata bisa haɗin kai da goyon bayan da suke bayarwa, tare da jaddada aniyarta na ci gaba da samar da ingantattun ayyuka a dukkan matakan shirye-shiryen aikin Hajji.

