Close Menu
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • Hajj News
  • Global
  • Health
  • Nahcon
  • Picture Gallery
  • Opinion
  • Videos
  • HAUSA
Facebook X (Twitter) Instagram
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram
SUBSCRIBE
  • Home
  • Hajj News

    975 Kwara Pilgrims Airlifted for 2025 Hajj

    May 15, 2025

    First Hajj Pilgrims Arrive by Sea at Jeddah Islamic Port

    May 15, 2025

    Nigerian Pilgrims Begin Second Phase of 2025 Hajj Journey – By Aminu Kabir Muhammad

    May 14, 2025

    Niger State’s First Batch of Pilgrims Set for Airlift to Saudi Arabia

    April 30, 2025

    Jigawa Governor Appoints Emir of Kazaure as Amirul Hajj for 2025

    April 29, 2025
  • Global

    flyadeal Aims To Serve 75,000 International Hajj Pilgrims In 2025

    January 23, 2025

    Reflections on the 4th Hajj Conference and Exhibition in Jeddah – By Muhammad Ahmad Musa

    January 21, 2025

    Hajj and Umrah Expo 2025: Innovation and Collaboration Take Center Stage in Jeddah – By Fatima Sanda Usara

    January 14, 2025

    Makkah Red Crescent Boosts Preparedness to Heavy Rainfall

    January 6, 2025

    Intense Rainfall Sweeps Through Makkah, Madina and Jeddah

    January 6, 2025
  • Health

    Gombe Muslim Pilgrim Board Commences Vaccination for 2025 Hajj Pilgrims – By Abdulqadir Aliyu Shehu

    April 28, 2025

    NAHCON Inaugurates Committee To Review National Medical Team Guidelines for Hajj 2025

    December 19, 2024

    Saudi Health Minister Strengthen Ties With Greece On Health Cooperation During Official Visit

    November 23, 2024

    Umm Al-Qura University volunteers extend help to pilgrims in Mina during Tashreeq

    June 17, 2024

    Hajj 2024: African pilgrim airlifted for emergency care

    June 14, 2024
  • Nahcon

    NAHCON Intensifies Efforts in Makkah to Fast-Track Nusuk Card Distribution for Nigerian Pilgrims

    May 22, 2025

    NAHCON Chairman Tasks Media Team on Fair, Responsible Coverage of 2025 Hajj

    May 20, 2025

    NAHCON Steps Up Oversight of Tour Operators’ Catering Ahead of 2025 Hajj

    May 19, 2025

    NAHCON Chairman Applauds Madinah Operations Team, Hails Stakeholder Collaboration

    May 18, 2025

    NAHCON Ensures Quality Feeding for Over 17,000 Nigerian Pilgrims in Madinah – By Ahmad Mu’azu

    May 16, 2025
  • Picture Gallery
  • Opinion

    Exposing Leadership Newspaper’s many lies against NAHCON chairman – By Ahmad Shafi’i PhD

    May 8, 2025

    What Do the Enemies of NAHCON Chairman Really Want? 

    May 3, 2025

    Who Will Now Thank the NAHCON Chairman? By Assalafy Yola

    April 29, 2025

    Hajj Commission, Professor Abdallahi Saleh, VP Shettima and the Daily Nigerian Report – By Uncle Anas Dukura

    April 18, 2025

    Who Is After the NAHCON Chairman? By Assalafy Yola

    April 9, 2025
  • Videos
  • HAUSA
HAJJ CHRONICLES
Home » Hajji 2025: Kungiyar Fararen Hula Ta Yi Kira Ga Gwamnoni Su Mayar Da Hankali Kan Fayil Din Harkokin Hajji
Hausa

Hajji 2025: Kungiyar Fararen Hula Ta Yi Kira Ga Gwamnoni Su Mayar Da Hankali Kan Fayil Din Harkokin Hajji

adminBy adminOctober 23, 2024No Comments3 Mins Read
Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Email Telegram
news6710a19b07f6a
news6710a19b07f6a

Dangane da jinkirin wajen sanar da fara rijistar maniyyata da wasu hukumomin jin dadin Alhazai na Jihohi da suke yi, kungiyar masu bayar da rahotanni da sa ido kan harkokin Hajji da Umrah ta Najeriya mai zaman kanta,ta yi kira ga Gwamnonin Jihohin da su baiwa al’amuran Hajji fifiko a Jihohinsu.

 

“Ya zuwa lokacin rubuta wannan labari, Jihohin Neja, Sokoto da Borno har yanzu ba su fara aikin rajistar ba duk da cewa sun samu umarnin Hukumar Alhazai ta Najeriya (NAHCON) a watan Agusta na cewa Jihohin su fara rajista.

 

“Muna sane da cewa har yanzu wasu Sakatarorin zartarwa na Hukumar Jin Dadin Alhazai Musulmi ba su mika rahoton aikin Hajjin 2024 ga Gwamnoninsu ba, wanda a sakamakon haka har yanzu ba su samu amincewar fara rajistar maniyyata daga shugabanninsu ba,” in ji IHR. a wata sanarwa mai dauke da sa hannun kodinetan ta na kasa, Ibrahim Mohammed, ranar Laraba.

 

Kungiyar ta fararen hula ta kuma nuna damuwarta kan yadda har yanzu ba a fara rijistar wasu jihohi ba ko da ana sa ran za su mika kaso na farko na kudaden ajiyar maniyyata zuwa hukumar NAHCON, tun daga ranar 2 ga watan Oktoba (kamar yadda kalandar hukumar NAHCON ta 2025 ta nuna) don isarwa ga kamfanonin don biyan kudin tantina a Mina.

 

“Cewa Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jiha za ta bukaci wata amincewa ta daban daga Gwamnonin Jihohi don fara rajistar maniyyata ko da bayan an ba su izini daga hukumar kula da aikin hajji, wani shiri ne na musamman na hadin gwiwa ga masana’antar Hajji wanda ke bukatar mafita cikin gaggawa”.

 

Kungiyar ta ce “Ya zama dole a lura cewa a ranar 23 ga watan Oktoba ma’aikatar aikin Hajji ta Saudiyya ta fara raba tanti ga kasashen da suea halartar aikin Hajji da suka biya.

 

 

 

“Duk wani sakataren zartarwa na Hukumar Jin Dadin Alhazai Musulmai na Jiha wanda bai gabatar da rahoton aikin Hajjin na 2024 watanni hudu bayan aikin Hajjin 2024 ba to a cire shi tare da maye gurbinsa da wanda ya cancanta,” in ji kungiyar.

 

Sannan kuma ya tunatar da gwamnonin jihohin cewa jinkirin fara rajistar maniyyata da Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihohi ke yi, shi ne ummul haba’isin matsalar rashin hidima da alhazan Najeriya ke fuskanta duk shekara a Saudiyya.

 

“Yin ragistar a makare yana haifar da jinkirin tura asusun rijistar maniyyata zuwa NAHCON, wanda hakan ya shafi gazawar hukumar wajen biyan kudade ga kamfanoni dake yin hidima ga alhazai da ke Saudiyya a daidai lokacin da zasu bad a damar yin isassun shirye-shirye don samar da ingantacciyar hidima ga maniyyatanmu.

 

“Ma’aikatan gudanarwa na jihohi na kawo cikas sosai wajen aiwatar da kalandar Hajji, don haka akwai bukatar a yi wani abu don yin daidai da dokar kafa hukumar NAHCON ta shekarar 2006, don baiwa maniyyatan jihohi damar fara rajista da wuri ba tare da jiran amincewar shugabannin zartarwa na jiha ba.

 

“Aikin Hajji al’amari ne na duniya wanda ake sa ran sama da kasashe 162 da ke halartar taron za su aiwatar a lokaci daya da aka fitar duk shekara kamar yadda ma’aikatar aikin Hajji ta Saudiyya ta fitar don zama taswirar jagora don shirye-shiryen aikin Hajji,” in ji kungiyar

Hajj 2025 IHR NAHCON Ragistar Aikin Haji
Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp

Related Posts

NAHCON Intensifies Efforts in Makkah to Fast-Track Nusuk Card Distribution for Nigerian Pilgrims

May 22, 2025

NAHCON Chairman Tasks Media Team on Fair, Responsible Coverage of 2025 Hajj

May 20, 2025

NAHCON Steps Up Oversight of Tour Operators’ Catering Ahead of 2025 Hajj

May 19, 2025
Leave A Reply Cancel Reply

Don't Miss
Nahcon

NAHCON Intensifies Efforts in Makkah to Fast-Track Nusuk Card Distribution for Nigerian Pilgrims

By adminMay 22, 20250

With the Tashriq days fast approaching, the National Hajj Commission of Nigeria (NAHCON) has stepped…

NAHCON Chairman Tasks Media Team on Fair, Responsible Coverage of 2025 Hajj

May 20, 2025

NAHCON Steps Up Oversight of Tour Operators’ Catering Ahead of 2025 Hajj

May 19, 2025

Governor Inuwa Yahaya Bids Farewell to First Batch of Gombe Pilgrims for 2025 Hajj – By Abdulkadir Aliyu Shehu

May 19, 2025
Stay In Touch
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • WhatsApp
Our Picks

NAHCON Intensifies Efforts in Makkah to Fast-Track Nusuk Card Distribution for Nigerian Pilgrims

May 22, 2025

NAHCON Chairman Tasks Media Team on Fair, Responsible Coverage of 2025 Hajj

May 20, 2025

NAHCON Steps Up Oversight of Tour Operators’ Catering Ahead of 2025 Hajj

May 19, 2025

Governor Inuwa Yahaya Bids Farewell to First Batch of Gombe Pilgrims for 2025 Hajj – By Abdulkadir Aliyu Shehu

May 19, 2025
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
© 2025HAJJ CHRONILES

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.