Close Menu
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • Hajj News
  • Global
  • Health
  • Nahcon
  • Picture Gallery
  • Opinion
  • Videos
  • HAUSA
Facebook X (Twitter) Instagram
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram
SUBSCRIBE
  • Home
  • Hajj News

    2026/1447 Hajj Preparations Officially Launched as NAHCON Joins Global Pilgrimage Community in Closing Ceremony

    June 9, 2025

    No Lives Lost in Makkah Fire, Senate Foreign Affairs Committee Confirms

    June 9, 2025

    Pilgrimage and Leadership: How Governor Inuwa Yahaya Stood Tall Among His Peers During the 2025 Hajj – Abdulkadir Aliyu Shehu

    June 8, 2025

    From Crisis to Victory: NAHCON Chairman Called to Prostrate in Thanks for 2025 Hajj Breakthrough – By Shamwil Isah

    June 8, 2025

    Governor Abba Yusuf Disburses ₦361 Million Support to Kano Pilgrims in Mina

    June 8, 2025
  • Global

    Indonesia Plans to Acquire Land for Hajj Village Near Makkah’s Grand Mosque

    July 31, 2025

    Egypt To Halt Land Hajj Trips by 2026 Over Saudi Transport Policy Changes

    July 31, 2025

    UAE Unveils Streamlined Hajj 2026 Accreditation Process to Ensure Transparency and Quality

    July 24, 2025

    flyadeal Aims To Serve 75,000 International Hajj Pilgrims In 2025

    January 23, 2025

    Reflections on the 4th Hajj Conference and Exhibition in Jeddah – By Muhammad Ahmad Musa

    January 21, 2025
  • Health

    Gombe Muslim Pilgrim Board Commences Vaccination for 2025 Hajj Pilgrims – By Abdulqadir Aliyu Shehu

    April 28, 2025

    NAHCON Inaugurates Committee To Review National Medical Team Guidelines for Hajj 2025

    December 19, 2024

    Saudi Health Minister Strengthen Ties With Greece On Health Cooperation During Official Visit

    November 23, 2024

    Umm Al-Qura University volunteers extend help to pilgrims in Mina during Tashreeq

    June 17, 2024

    Hajj 2024: African pilgrim airlifted for emergency care

    June 14, 2024
  • Nahcon

    Saudi Extends Data Capture Deadline as NAHCON Chairman Resigns

    February 10, 2026

    Saudi Ministry Closes 2026 Hajj Data Capture; NAHCON Seeks Extension, Warns Pilgrims on Payments

    February 9, 2026

    Deadline for Pilgrims’ Data Capturing Remains 8th February 2026 – NAHCON

    February 5, 2026

    No Hajj Without Permit (Visa), Saudi Minister affirms – By Mariam Zubair

    February 5, 2026

    NAHCON Chairman Hails Saudi-Nigeria Hajj Ties as Saudi Minister Visits Abuja – By Jamilu Adam

    February 3, 2026
  • Picture Gallery
  • Opinion

    NAHCON Reconciliation Viewed as Positive Step for Hajj Administration – By Muhammad Sulaiman Gama

    February 2, 2026

    NAHCON Board’s Vote of No Confidence: A Mask for Self-Interest.

    February 1, 2026

    Nigeria Hajj Industry: When Would Pilgrims’ Interest Supercede Personal Interest of Handlers and Stakeholders

    January 31, 2026

    Who Is Afraid of Pakistan? By Faruku Umar

    January 31, 2026

    Why Kano Cannot Afford Delay in Appointing a New CEO for the Pilgrims Welfare Board – By Jamilu Adam

    January 28, 2026
  • Videos
  • HAUSA
HAJJ CHRONICLES
Home » Saudia ta Ƙara Wa’adin Cike Bayanan Maniyyata, Yayin Da Shugaban NAHCON ya Yi Murabus
Hausa

Saudia ta Ƙara Wa’adin Cike Bayanan Maniyyata, Yayin Da Shugaban NAHCON ya Yi Murabus

adminBy adminFebruary 10, 2026Updated:February 10, 2026No Comments3 Mins Read
Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Email Telegram
FB IMG 1766066402041

Ma’aikatar Hajji da Umrah ta Ƙasar Saudiyya ta ƙara wa’adin cike bayanan alhazai da kuma tsara rukunan alhazai domin Hajjin shekarar 2026.

A sanarwar da mataimakiyar Daraktar yada da hulda da Jama’a ta Hukumar Fatima Sanda Usara ta fitar, tace bisa umarnin Mataimakin Shugaban Ƙasa na Tarayyar Najeriya, Sanata Kashim Shettima, Ministan Harkokin Waje, Ambasada Yusuf Maitama Tugga, ya tuntuɓi hukumomin Saudiyya domin neman ƙarin lokaci na musamman ga Najeriya don kammala cike bayanan alhazai. Hukumomin Saudiyya sun amince da wannan buƙata cikin karamci.

Sai dai ana sa ran cewa bayan ƙarewar wannan ƙarin lokaci, hukumomin Saudiyya ba za su sake amincewa da wani ƙarin lokaci ba, tare da jaddada muhimmancin gaggauta kammala aikin.

Don haka, an shawarci masu kula da harkokin Hajji da su yi aiki dare da rana domin tabbatar da kammala wannan aiki cikin gaggawa.

Wannan ƙarin lokaci ya zo ne ƙasa da awanni 48 bayan rufe dandalin Nusuk Masar na cike bayanai a duniya baki ɗaya.

Cikin sanarwar, an buƙaci hukumomin Hajji da su “kammala dukkan bayanan alhazai da ake buƙata cikin gaggawa domin kauce wa matsaloli a minti na ƙarshe.”

A wani labarin kuma, tsohon Shugaban Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON), Farfesa Abdullahi Saleh Usman, ya nuna godiyarsa ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da Mataimakin Shugaban Ƙasa Sanata Kashim Shettima bisa damar da aka ba shi na jagorantar NAHCON.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da ya fitar a yau, 10 ga Fabrairu, 2026, inda ya bayyana cewa murabus ɗin nasa ya fara aiki daga Litinin, 9 ga Fabrairu, 2026.

An miƙa takardar murabus ɗin a rubuce ga Mai Girma Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, GCFR, bisa tanadin Sashe na 3(6) na Dokar Kafa Hukumar Alhazai ta Ƙasa ta 2006.

Farfesa Usman ya bayyana cewa dalilai na kashin kai, bayan nazari da addu’a, su ne suka sa ya yi murabus.

Ya kuma jaddada cewa murabus ɗin ba shi da alaƙa da rashin gamsuwa da Hukumar, Gwamnatin Tarayya, ko aikin NAHCON.

Farfesa Abdullahi Saleh Usman ya karɓi ragamar shugabancin NAHCON daga Malam Jalal Arabi a ranar 20 ga Agusta, 2024, a matsayin mukaddashi, kafin Majalisar Dattawa ta tabbatar da shi a matsayin cikakken Shugaban Hukumar a ranar 10 ga Oktoba, 2024.

Yana da digirin farko daga Jami’ar Madina, digirin digirgir a fannin Nazarin Addinin Musulunci daga Jami’ar Peshawar da ke Pakistan, da kuma digirin digirgir (PhD) a Nazarin Addinin Musulunci daga Jami’ar Usmanu Danfodiyo, Sokoto.

Farfesa Usman ya taɓa zama Shugaban Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano, kuma fitaccen malamin addinin Musulunci ne.

Gudanarwa da ma’aikatan NAHCON sun yaba da gudunmawar Farfesa Usman ga alhazan Najeriya da sauran masu ruwa da tsaki.

Hukumar NAHCON ta tabbatar da kudurinta na ci gaba da samar da ingantattun ayyuka masu sauƙi da mayar da hankali ga jin daɗin alhazai, tare da shirye-shiryen tabbatar da nasarar gudanar da Hajjin 2026.

Maniyyata Murabus Saudi Shugaban NAHCON
Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp

Related Posts

Saudi Extends Data Capture Deadline as NAHCON Chairman Resigns

February 10, 2026

Shugaban NAHCON Abdullahi Saleh Usman Ya Yi Murabus

February 10, 2026

Hukumar Alhazai ta Sokoto ta Kammala Ɗora Bayanan Mahajjata 2,403 a Manhajar E-Track Masar

February 10, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

Don't Miss
Hausa

Saudia ta Ƙara Wa’adin Cike Bayanan Maniyyata, Yayin Da Shugaban NAHCON ya Yi Murabus

By adminFebruary 10, 20260

Ma’aikatar Hajji da Umrah ta Ƙasar Saudiyya ta ƙara wa’adin cike bayanan alhazai da kuma…

Saudi Extends Data Capture Deadline as NAHCON Chairman Resigns

February 10, 2026

Shugaban NAHCON Abdullahi Saleh Usman Ya Yi Murabus

February 10, 2026

Hukumar Alhazai ta Sokoto ta Kammala Ɗora Bayanan Mahajjata 2,403 a Manhajar E-Track Masar

February 10, 2026
Stay In Touch
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • WhatsApp
Our Picks

Saudia ta Ƙara Wa’adin Cike Bayanan Maniyyata, Yayin Da Shugaban NAHCON ya Yi Murabus

February 10, 2026

Saudi Extends Data Capture Deadline as NAHCON Chairman Resigns

February 10, 2026

Shugaban NAHCON Abdullahi Saleh Usman Ya Yi Murabus

February 10, 2026

Hukumar Alhazai ta Sokoto ta Kammala Ɗora Bayanan Mahajjata 2,403 a Manhajar E-Track Masar

February 10, 2026
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
© 2026HAJJ CHRONILES

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.