Close Menu
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • Hajj News
  • Global
  • Health
  • Nahcon
  • Picture Gallery
  • Opinion
  • Videos
  • HAUSA
Facebook X (Twitter) Instagram
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram
SUBSCRIBE
  • Home
  • Hajj News

    Mahmoud Flags Off First Batch of FCT Pilgrims for 2026 Hajj

    May 7, 2026

    Saudi Hajj Ministry Warns Pilgrims Against Unauthorized Permits

    May 7, 2026

    Hajj 2026: Saudi Arabia Expands Cooling and Shade Facilities in Arafat

    May 5, 2026

    1,357 Pakistani Pilgrims Arrive in Madinah as Hajj 2026 Airlift Commences

    April 20, 2026

    Hajj 2026: Saudi Arabia Plans Massive Airlift with 12,000+ Flights for Pilgrims

    April 20, 2026
  • Global

    Indonesia Plans to Acquire Land for Hajj Village Near Makkah’s Grand Mosque

    July 31, 2025

    Egypt To Halt Land Hajj Trips by 2026 Over Saudi Transport Policy Changes

    July 31, 2025

    UAE Unveils Streamlined Hajj 2026 Accreditation Process to Ensure Transparency and Quality

    July 24, 2025

    flyadeal Aims To Serve 75,000 International Hajj Pilgrims In 2025

    January 23, 2025

    Reflections on the 4th Hajj Conference and Exhibition in Jeddah – By Muhammad Ahmad Musa

    January 21, 2025
  • Health

    Gombe Commences Vaccination of 965 Pilgrims Ahead of 2026 Hajj- By Abdulkadir Aliyu

    April 25, 2026

    Gombe Muslim Pilgrim Board Commences Vaccination for 2025 Hajj Pilgrims – By Abdulqadir Aliyu Shehu

    April 28, 2025

    NAHCON Inaugurates Committee To Review National Medical Team Guidelines for Hajj 2025

    December 19, 2024

    Saudi Health Minister Strengthen Ties With Greece On Health Cooperation During Official Visit

    November 23, 2024

    Umm Al-Qura University volunteers extend help to pilgrims in Mina during Tashreeq

    June 17, 2024
  • Nahcon

    NAHCON Mourns Loss of Adamawa Pilgrim, Malama Aishatu Muhammadu

    May 10, 2026

    NAHCON Clarifies Ogun Pilgrims’ Airlift- Gateway Airport Not Rejected by Flynas – NAHCON Chairman

    May 8, 2026

    NAHCON Assures Pilgrims as 9,756 Nigerians Arrive Madinah for Hajj 2026

    May 7, 2026

    NAHCON Launches “Hajj Companion App” to Support Nigerian Pilgrims

    May 5, 2026

    FG Weighs Policy Options to Cushion Aviation Fuel Costs, Assures Seamless 2026 Hajj Airlift

    April 30, 2026
  • Picture Gallery
  • Opinion

    Gov Ahmad Aliyu and His Transformational Contributions to Hajj Administration in Sokoto

    March 23, 2026

    Nigeria Hajj Industry: Back To Square One – By Abubakar Jidda Usman

    February 11, 2026

    NAHCON Reconciliation Viewed as Positive Step for Hajj Administration – By Muhammad Sulaiman Gama

    February 2, 2026

    NAHCON Board’s Vote of No Confidence: A Mask for Self-Interest.

    February 1, 2026

    Nigeria Hajj Industry: When Would Pilgrims’ Interest Supercede Personal Interest of Handlers and Stakeholders

    January 31, 2026
  • Videos
  • HAUSA
HAJJ CHRONICLES
Home » Gwamna Aliyu Ya Yi Bankwana Da Rukuni Na Farko Na Alhazan Sakkwato
Hausa

Gwamna Aliyu Ya Yi Bankwana Da Rukuni Na Farko Na Alhazan Sakkwato

adminBy adminMay 11, 2026No Comments2 Mins Read
Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Email Telegram
Saudi Hajj Ministry Warns Pilgrims Against Unauthorized Permits 20260511 100930 0000

Gwamnan Jihar Sakkwato, Mai Girma Dakta Ahmad Aliyu Sokoto, ya yi bankwana da rukuni na farko na maniyyatan jihar da za su tafi aikin Hajjin shekarar 2026 zuwa Ƙasar Saudiyya mai tsarki.

 

A cewar Shugaban Sashen Yaɗa Labarai da Sadarwa na Hukumar, Faruku Umar, taron bankwanar wanda ya gudana a Filin Jirgin Sama na Sultan Abubakar III da ke Sakkwato, ya samu halartar Amirul Hajj na Jihar kuma Shugaban Tawagar Gwamnatin Jiha, Ministan Kwadago da Samar da Ayyukan Yi na Ƙasa, Alhaji Muhammad Maigari Dingyadi, Babban Sakataren Hukumar Alhaji Ibrahim Umar JJ, jami’an gwamnati da kuma mambobin gudanarwar Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar.

 

Gwamnan wanda Mataimakinsa, Alhaji Idris Muhammad Gobir, ya wakilta, ya taya maniyyatan murnar kasancewa cikin waɗanda Allah Maɗaukakin Sarki Ya zaɓa domin gudanar da wannan ibada mai tsarki a bana.

 

A jawabin bankwanarsa, Gwamna Ahmad Aliyu ya buƙaci alhazan da su zama jakadu nagari na Jihar Sakkwato da Najeriya ta hanyar nuna ɗa’a, haƙuri da tsoron Allah a tsawon zamansu a ƙasa mai tsarki.

 

Ya kuma shawarce su da su kasance masu bin doka da oda, su mutunta ƙa’idoji da dokokin da aka tsara domin gudanar da aikin Hajji, tare da mayar da hankali wajen yin addu’o’i domin zaman lafiya, haɗin kai da ci gaban Jihar Sakkwato da Najeriya baki ɗaya.

 

Gwamnan ya ƙara da tabbatar wa alhazan cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da bayar da cikakken goyon baya domin tabbatar da gudanar da aikin Hajji cikin nasara da kwanciyar hankali, tare da yabawa Hukumar Jin Daɗin Alhazan ta Jihar Sakkwato bisa shirye-shiryen da ta yi domin jin daɗi da walwalar alhazan.

 

Ya kuma roƙi Allah Ya ba su kariya da jagora, tare da yi musu fatan tafiya lafiya da kuma nasarar sauke farali.

 

Tun da fari, Amirul Hajj na Hajjin 2026 kuma Ministan Kwadago da Samar da Ayyukan Yi, Alhaji Muhammad Maigari Dingyadi, ya taya maniyyatan murnar samun damar gudanar da aikin Hajji.

 

Ya buƙace su da su kasance masu haɗin kai, haƙuri da fahimtar juna a lokacin gudanar da aikin Hajjin, tare da bin umarnin jami’ai da hukumomin Saudiyya domin samun nasarar aikin.

 

Amirul Hajj ɗin ya kuma roƙi alhazan da su yi addu’o’i sosai domin Jihar Sakkwato, Najeriya da shugabanninta, tare da yi musu fatan tafiya lafiya da Hajji karɓaɓɓe.

Alhazan Sokoto Bankwana Gwamna Aliyu
Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp

Related Posts

Hajin 2026: Uwa ‘Yar Malaysia Ta Baiwa Danta Kyautar Zuwa Hajji Bayan Shekaru na Tanadi

May 4, 2026

An Kammala Bitar Alhazai a Kano, Jigilar Maniyyata za ta Fara 14 ga Mayu

May 4, 2026

Hajjin 2026: Sama da Ma’aikatan Lafiya 700 da Motocin Asibiti 90 Sun Shirya a Madinah

May 2, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

Don't Miss
Hausa

Gwamna Aliyu Ya Yi Bankwana Da Rukuni Na Farko Na Alhazan Sakkwato

By adminMay 11, 20260

Gwamnan Jihar Sakkwato, Mai Girma Dakta Ahmad Aliyu Sokoto, ya yi bankwana da rukuni na…

Governor Aliyu Bids Farewell To First Batch of Sokoto Pilgrims

May 11, 2026

NAHCON Mourns Loss of Adamawa Pilgrim, Malama Aishatu Muhammadu

May 10, 2026

Governor Yusuf Approves 200 Riyals Support, Ihram for Each Kano Pilgrim

May 10, 2026
Stay In Touch
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • WhatsApp
Our Picks

Gwamna Aliyu Ya Yi Bankwana Da Rukuni Na Farko Na Alhazan Sakkwato

May 11, 2026

Governor Aliyu Bids Farewell To First Batch of Sokoto Pilgrims

May 11, 2026

NAHCON Mourns Loss of Adamawa Pilgrim, Malama Aishatu Muhammadu

May 10, 2026

Governor Yusuf Approves 200 Riyals Support, Ihram for Each Kano Pilgrim

May 10, 2026
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
© 2026HAJJ CHRONILES

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.